Karin Bayani: Zanga-Zanga Ta Ɓarke a Gidan Gwamnatin Jihar PDP Kan Muhimman Abu 8
- Shiga tsakanin da Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi a rikicin jihar Ribas ya bar baya da ƙura
- Ɗaruruwan masu zanga-zanga sun mamaye gidan gwamnatin jihar da ke Fatakwal ranar Jumu'a domin nuna adawa da yarjejeniya 8
- Zanga-zangar na zuwa ne bayan bidiyon kwamishinan ayyuka ya yaɗu inda aka ji yana cewa Tinubu ya tilasta wa Fubara sa hannu kan yarjejeniyar
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Rivers - Gagarumar zanga-zanga ta ɓarke a Fatakwal, babban birnin jihar Ribas ranar Jumu'a, 22 ga watan Disamba, 2023.
Zanga-zangar ta ɓalle ne kan sulhun da shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi a rikicin siyasar da ya dabaibaye jihar, wanda a karshe aka cimma yarjejeniya 8.

Kara karanta wannan
Shugaba Tinubu, Zulum da wasu manyan ƙusoshi da zasu halarci gasar karatun Alqur'ani Mai Girma

Asali: Twitter
A cewar rahoton Daily Trust, zanga-zangar ta nuna goyon baya ce ga Gwamna Siminalayi Fubara.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Jerin waɗanda suka shiga wannan zanga-zanga
Bayanai sun nuna cewa masu zanga-zangar sun kunshi ɗalibai, ƙungiyoyin fararen hula, kungiyoyin kwadago da kuma wasu Hausawa mazauna jihar Ribas.
Tun da duku-duku, misalin karfe 7:00 na safiyar yau Jumu'a, tulin masu zanga-zangar suka mamaye gidan gwamnati da ke titin Azikwe a Fatakwal.
An ga masu zanga-zangar suna taruwa a wasu rumfuna da aka kafa a ƙofar shiga gidan gwamnatin, inda suka nuna adawa da yarjejeniya 8 da Fubara ya rattaɓa wa hannu.
Ko menene ya haddasa zanga-zangar?
Wannan na zuwa ne awanni 24 bayan tsohon kwamishinan ayyuka na jihar, David Briggs, ya zargi Shugaba Tinubu da tilastawa Gwamna Fubara ya sa hannu a yarjejeniyar.
A wani bidiyo da Legit Hausa ta gani, Briggs ya yi ikirarin cewa yana ɗaya daga cikin masu ruwa da tsakin da suka halarci taron da aka yi a fadar shugaban ƙasa ranar Litinin.

Kara karanta wannan
Daga Karshe, yan majalisar dokoki sun ɗauki sabon mataki ƙan yunkurin tsige gwamnan PDP
Tsohon kwamishinan ya shaida wa manema labarai cewa Gwamna Fubara ya sa hannu kan yarjejeniyar ne bisa tursasawar da aka masa.
A cewarsa, duk masu zargin gwamnan ya kamata su binciki asalin mai ya faru a fadar shugaban ƙasa, kamar yadda Punch ta ruwaito.
Ya ce Shugaba Tinubu ya zo da rubutacciyar yarjejeniya, yana cewa wannan takarda ce matsayar shugaban ƙasa.
Asali: Legit.ng