Gwamnan APC Zai Yi Murabus Daga Madafun Iko Kan Rashin Lafiya? Gaskiya Ta Bayyana

Gwamnan APC Zai Yi Murabus Daga Madafun Iko Kan Rashin Lafiya? Gaskiya Ta Bayyana

  • Har yanzu ana ta takaddama kan yanayin rashin lafiyar Gwamna Rotimi Akeredolu na jihar Ondo
  • Yayin da wasu ke ganin ya kamata ya yi murabus saboda rashin lafiya, Gwamnatin Ondo ta ce gwamna na yin aikinsa
  • Kwamishinar yaɗa labarai ta ce har yanzun gwamnan bai gaza aiki ba, kawai ya daina halartar taruka da bukukuwa ne

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Ondo - Kwamishinar yada labarai da wayar da kan jama’a a jihar Ondo, Mis Bamidele Ademola-Olateju, ta bayyana dalilin da ya sa Gwamna Rotimi Akeredolu (SAN) ba zai yi murabus ba.

Wannan na zuwa ne yayin da masu ruwa da tsaki a jihar suka buƙaci gwamnan ya yi murabus ko ya miƙa karfin iko ga mataimakinsa saboda rashin lafiyar da yake fama da ita.

Kara karanta wannan

Gwamna Uba Sani ya ɗauki wasu muhimman matakai masu kyau kan jefa wa Musulmi bam a Tudun Biri

Gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu.
Ondo: Dalilin da Ya Sa Gwamna Akeredolu Ba Zai Yi Murabus Ba, Kwamishina Hoto: Rotimi Akeredolu
Asali: Facebook

Amma kwamishinar yaɗa labaran ta ce har yanzun Gwamna Akeredolu bai gaza ba duk da rashin lafiyar da yake fama da ita, don haka babu buƙatar ya yi murabus.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ademola-Olateju ta yi wannan bayani ne a wata hira da ta yi da Arise tv da safiyar ranar Jumu'a, 8 ga watan Disamba, 2023

Har yanzu dai batun lafiyar gwamnan na ci gaba da jan hankali da haddasa kace-nace musamman saboda yadda ya koma zama a gidansa na kai da kai da ke Ibadan a jihar Oyo.

Gwamnan ya ci gaba da zama a Ibadan tun lokacin da ya dawo daga ƙasar Jamus a watan Satumba, bayan shafe sama da watanni uku yana jinya, cewar Daily Trust.

Meyasa gwamnan ba zai yi murabus ba?

Da take jawabi kan batun rashin lafiyar, kwamishinar yaɗa labaran ta ce har yanzu gwamnan yana ayyukan da suka rataya a wuyansa bai gaza ba.

Kara karanta wannan

Kaduna: Gwamna Sani ya caccaki kalaman DHQ kan dalilin jefa bam a taron Musulmai, ya nemi abu 1

A cewarta, abubuwan da za a iya cewa Gwamna Akeredolu ba ya gaza yi a yanzu ba su wuce halartar taruka da bukukuwa na yau da kullum kamar ɗaurin aure ba.

Da aka tambaye ta ko Akeredolu ya yi tunanin murabus kamar yadda lokacin yana shugaban ƙungiyar lauyoyi (NBA) ya nemi marigayi Umaru Yar’Adua ya yi murabus, kwamishinar ta ce:

"Gwamna bai gaza ba, har yanzu ina nan a kan bakata, yana yin abin da ya kamata cikin sauki, babu wata matsala, kawai siyasa ce ta sa ake kambama abun."

NNPP da APC sun rattaɓa hannu kan yarjejeniya a Kano

A wani rahoton na daban Manyan jam'iyyu biyu masu adawa da juna a jihar Kano, NNPP da APC sun sake sa hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.

Jam'iyyun biyu sun yi haka ne ranar Jumu'a domin tabbatar da zaman lafiya gabanin, lokacin da kuma bayan hukuncin kotun koli.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel