Wakilan APC da Accord Party Sun Bai Wa Hammata Iska a Cibiyar Tattara Kuri’an Zaben Gwamnan Bayelsa

Wakilan APC da Accord Party Sun Bai Wa Hammata Iska a Cibiyar Tattara Kuri’an Zaben Gwamnan Bayelsa

  • Wakilan jam'iyyun APC da Accord sun bai wa hamata iska yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon zaben jihar Bayelsa
  • Wakilin jam'iyyar Accord Victor Werinepere-Fisi ya naushi takwaransa na APC, Dakta Dennis Otiotio wamda hakan ya jawo dakatar da shirin
  • Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon zaben da Gwamna Diri ke kan gaba a zaben

Abdullahi Abubakar, kwararren editan siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Bayelsa - Yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon zaben jihar Bayelsa, jam'iyyun APC da Accord sun bai wa hamata iska.

Wakilan jam'iyyun sun doku ne a dakin taron da ake tattara sakamakon zaben inda suka ta da hankulan mutane, cewar Channels TV.

Kara karanta wannan

Yanzu yanzu: Ajaka na SDP ya nemi a soke zaben gwamna a Kogi ta tsakiya

Wakilan APC da Accord sun doku a dakin tattara sakamakon zaben jihar Bayelsa
Ana ci gaba da samun tsaiko yayin tattara sakamakon zaben jihar Bayelsa. Channels TV.
Asali: Twitter

Mene dalilin jawo rikicin tsakanin APC da Accord?

Lamarin ya faru ne a yau Litinin 13 ga watan Nuwamba a Yenagoa babban birnin jihar Bayelsa, cewar Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tattara sakamakon wanda mataimakan shugaban Jami'ar Fasaha da ke Minna, Farfesa Faruk Kuta ke jagorancinta an fara ne da misalin karfe 12.

Wannan rikici na wakilan biyu ya kawo cikas a dakin tattara sakamakon zaben wanda sai da aka fitar da su daga ciki.

Wane mataki aka dauka kan rikicin a Bayelsa?

Har ila yau, dalilin wannan rikici an dage ci gaba da tattara sakamakon a wannan lokaci saboda samun daidaito na tsaro, Politics Nigeria ta tattaro.

Wakilin jam'iyyar Accord a jihar, Mista Victor Werinepere-Fisi ya naushi takwaransa na APC, Dakta Denis Otiotio kan rashin jituwa a tsakani.

A yanzu haka an gama tattara sakamakon zaben kananan hukumomin jihar inda Gwamna Douye Diri na jam'iyyar PDP ke ba da ratar kuri'u sama da dubu 65 a zaben jihar.

Kara karanta wannan

INEC ta dage tattara sakamakon zaben gwamnan Bayelsa, cikakken bayani ya bayyana

Sylva ya sake lashe karamar hukuma a Bayelsa

A wani labarin, dan takarar jam'iyyar APC a zaben, Timipre Sylva ya sake lallasa Gwamna Douye Diri a karamar hukumar Brass da ke jihar.

Wannan na zuwa ne bayan Diri na jam'iyyar PDP na bai wa Sylva rata a zaben da aka gudanar a ranar Asabar 11 ga watan Nuwamba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.