Zaben Imo: Karin Jiga-Jigan PDP Sun Sauya Sheka Zuwa Jam'iyyar APC

Zaben Imo: Karin Jiga-Jigan PDP Sun Sauya Sheka Zuwa Jam'iyyar APC

  • Jam'iyyar APC ta ƙara kassara babbar jam'iyyar adawa PDP yayin da ake tunkarar zaben gwamna a jihar Imo
  • Tawagar ƙarin jiga-jigan mambobin PDP a yankin ƙaramar hukumar Ohaji-Egbema sun sauya sheƙa zuwa APC
  • Shugaban APC na jihar Imo ya ja hankalin masu sauya sheƙar su yi aiki tukuri domin nasarar gwamna Uzodinma a zabe na gaba

Jihar Imo - Jam'iyyar APC mai mulki ta ƙara maraba da sabbin mambobi yayin da jam'iyyar PDP ƙe ƙara rushe wa a garin Egbema, ƙaramar hukumar Ohaji-Egbema a jihar Imo.

The Nation ta tattaro cewa masu sauya sheƙar sun sha alwashin haɗa kai da sauran mambobin APC wajen goyon bayan tazarcen gwamna Hope Uzodinma a zaɓe mai zuwa.

Gungun mambobin PDP sun koma APC.
Zaben Imo: Karin Jiga-Jigan PDP Sun Sauya Sheka Zuwa Jam'iyyar APC Hoto: thenation
Asali: UGC

Hukumar zaɓe ta ƙasa INEC ta sanya ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023 domin gudanar da zaɓen gwamna a jihar Imo, Kogi da kuma Bayelsa, Channels tv ta rahoto.

Kara karanta wannan

Nasarar APC Ta Fara Tangal-Tangal, Kotun Zaɓe Ta Tanadi Hukunci Kan Zaben Gwamnan Arewa

Meyasa suka sauya sheka daga PDP zuwa APC?

Sun ƙara da bayanin cewa matakin barinsu PDP da shiga APC ya samo asali ne daga burinsu na ba da gudummuwa domin tabbatar da tazarcen gwamna mai ci.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Da yake jawabi ga sabbin mambobin daga Egbema, Mista Opiah ya tabbatar da cewa nan ba da dadewa ba wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP daga Ohaji-Egbema za su sauya sheka zuwa APC.

Ya ce:

"Akwai wadanda har yanzu suna ɗan kokwanto amma nan ba da jimawa ba za su yanke shawara. Burin mu ne mu ruguza jam’iyyar PDP a Ohaji-Egbema domin gwamna ya yi tazarce."

APC ta buƙaci aiki tukuru daga mambobin

Shugaban APC na Imo, Mcdonald Ebere, yayin da yake maraba da masu sauya shekar, ya bukace su da su yi aiki tukuru domin tabbatar da gwamna Uzodinma ya yi nasara.

Kara karanta wannan

"Ba Haka Ake Yi Ba": Hadimin Atiku Ya Caccaki Shugaba Tinubu, Ya Yi Masa Wani Muhimmin Gyara 1

Mista Ebere ya ce:

"Kuna ganin muna karbar ku ana cikin ruwan sama. Wannan ya nuna da gaske muke, a shirye muke mu karɓe ku a kowane lokaci. Ina rokon ku da ku yi aiki tukuri domin gwamna ya yi nasara."

Bola Tinubu Ya Nada Sabbin Shugabannin Hukumomi 2 Na Tarayya

A wani rahoton kun ji cewa Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗin Aliyu Tijani Ahmed a matsayin sabon shugaban hukumar kula da baƙi da 'yan gudun hijira ta ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta tabbatar da wannan naɗi ne a wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasa, Ajuri Ngelale, ya fitar ranar Alhamis, 14 ga watan Satumba, 2023.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262