Mai Neman Karbe Kujerar NNPP Ya Kunyata, Alkali Ya Ce a Biya ‘Dan Majalisa Kudi
- Kotun sauraron korafin zabe da ke Kano ta gagara rusa nasarar Sagir Koki (NNPP) a zaben 2023
- Alkalai sun ce Lauyoyin Muntari Ishaq Yakasai ba su zo da hujjojin da za a soke hukuncin INEC ba
- Kogi wanda yake Majalisar Tarayya ya samu N100, 000 a sakamakon karar da aka shigar a kan shi
DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!
Kano - Kotun sauraron korafin zaben Majalisar Tarayya mai zama a garin Kano ya yi watsi da karar da aka shigar a kan Sagir Koki (NNPP).
Punch ta ce Muntari Ishaq Yakasai bai yi nasara a yunkurinsa na karbe kujerar ‘dan majalisar wakilan tarayya daga hannun Sagir Koki ba.
A hukuncin da Alkalan kotun uku su ka zartar a karkashin jagorancin Flora Azinge, an tabbatar da raunin hujjojin lauyan Muntari Yakassai.
!['Yan NNPP a Kano 'Yan NNPP a Kano](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/a81c58094fbb28c1.jpg?imwidth=900)
Asali: Twitter
Babu hujjar magudin NNPP
![](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/d2e0eac33645a055.jpg?impolicy=cropped-image&imwidth=256)
Kara karanta wannan
Sharrin Shari'a: Sanatocin APC da Kotu Ta Kora Kafin a Cinye Albashin Wata 3 a Majalisa
Mai shari’a Azinge ta ce wanda ya shigar da kara bai iya gamsar da kotu cewa an yi aringizo wajen kada kuri’a a rumfuna 25 a mazabarsa ba.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Kotun sauraron karar zaben ya ce hujjojin da mai kara ya gabatar gaban kotu ba su isa ba, kuma ba su da karfin da za a iya rusa zabe da su.
Wani rahoton da aka fitar ya ce alkalan sun ce shaidun je-ka-nayi-ka ‘dan takaran na APC ya gabatar, wadanda su ka dogara da an ce-ka ce.
Alkalan sun zargi lauyoyin Muntari Yakassai da gabatar da wasu takardun da ba su da alaka da shari’ar zaben ‘dan majalisar tarayyan da ake yi.
Kotu tayi kaca-kaca da hujjojin APC
A shaidar da su ka gabatar, masu bada shaidar sun tabbatar da ba su rumfar zaben a wuraren da su ka ce an yi aringizon kuri’a.
![](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/914be44e490d4333.jpg?impolicy=cropped-image&imwidth=256)
Kara karanta wannan
Shugaban Majalisar Dattawa Ya Magantu Kan Hukuncin da Kotun Zabe Ta Yanke, Ya Fada Wa Atiku da Obi Mafita
Ba su dace a yarda da maganarsu ba. Babu wani mai bada shaidan da za ayi imani da shi daga bayanan da su ka gabatar kai-tsaye.
Sannan ya gabatar da takardun da ba su da alaka domin nuna an saba doka, an yi aringizo, kuma ba a bi dokar zabe ta shekarar 2022 ba.
Saboda haka an bada N100, 000 ga wanda aka yi kara, an watsar da korafin saboda rashin shaida.
- Flora Azinge
Shari'ar zaben 2023 a kotu
Ku na da labari Natasha Akpoti-Uduaghan ta karbe wurin Sanata Abubakar Sadiku-Ohere kuma PDP ta yi galaba kan Sanata Thomas Onowakpo.
Kotun sauraron karar zaben ‘Dan majalisar Kogi ta gabas a 2023 ta raba Sanatan APC da kujerarsa.
Asali: Legit.ng