Daga Karshe, Majalisar Dattawa Ta Yi Magana Kan Ministocin da Tinubu Zai Naɗa

Daga Karshe, Majalisar Dattawa Ta Yi Magana Kan Ministocin da Tinubu Zai Naɗa

  • Jinkirin shugaba Bola Tinubu wajen miƙa sunayen Ministoci ka iya tilasta wa majalisar dattawa ɗaga hutunta na shekara-shekara
  • A ranar 27 ga watan Yuli majalisar zata tafi hutu amma wata majiya daga majalisar dattawa ta ce ana sa ran isowar sunayen ministoci a farkon mako mai zuwa
  • Mai magana da yawun majalisar dattawa ya ce har yanzun ba a bayyana ranar da Sanatoci zasu tafi hutu ba, don haka ba dalilin musu kan batun

FCT Abuja - Da yiwuwar majalisar dattawa ta ɗage shirinta na tafiya hutun shekara yayin da ake tsammanin isowar sunayen ministocin shugaban ƙasa domin tantance wa.

A rahoton da jaridar The Nation ta tattara, Sanatoci na tsammanin shugaba Bola Ahmed Tinubu zai aiko da sunayen ministocin a farkon mako mai zuwa.

Kara karanta wannan

Su waye ministocin Tinubu? Jigon siyasa ya fadi dalilin jinkirin nada ministoci

Sanata Godswill Akpabio da Bola Ahmed Tinubu.
Daga Karshe, Majalisar Dattawa Ta Yi Magana Kan Ministocin da Tinubu Zai Naɗa Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Twitter

Meyasa Sanatoci zasu fasa tafiya hutu?

Ɗaya daga cikin shugabannin majalisar dattawa ya ce ana tsammanin Sanatoci zasu tafi hutunsu na shekara daga ranar 27 ga watan Yuli, 2023 zuwa watan Satumba.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Sai dai a cewarsa, mambobin majalisar dattawan a shirye suke su riƙa zama kowace rana domin tabbatar da sun tantance Ministocin da aka naɗa, koda hakan zai jawo ɗaga tafiya hutun da mako ɗaya.

Shugaban kwamitin yaɗa labarai na majalisar dattawa, Sanata Yemi Adaramodu, ya ce majalisar na da isasshen lokacin duba buƙatar shugaban kasa kafin tafiya hutu.

A cewarsa, har yanzu ba a sanar da ranar tafiya hutun shekara ba a majalisar dattawa, saboda haka tambaya kan yiwuwar ɗaga lokacin bata taso ba kwata-kwata.

Majalisar dattawa za ta yi nazari kan Ministocin Tinubu

A kalamansa ya ce:

"Akwai isasshen lokacin gabatar da sunayen ministocin da kuma tantance su."

Kara karanta wannan

Ina aka kwana: Magana ta kare, majalisa ta fasa zuwa hutu saboda rashin ministocin Tinubu

Adaramodu ya jaddada cewa majalisar tarayya zata yi abinda ya dace kuma ba zata yi kuskuren bai wa yan Najeriya kunya ba.

Rahotanni sun bayyana cewa shugaban ƙasa Tinubu ya tura sunayen ministocin ga hukumar yan sandan farin kaya (DSS) da hukumar yaƙi da rashawa (EFCC) domin tantance su.

"N8,000 Kudi Ne Masu Yawa" Gwaman Sule Ya Kare Tallafin Shugaba Tinubu

Kuna da labarin Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya ce N8,000 kuɗi masu yawa a wurin wasu iyalai da dama a Najeriya masu fama da talauci.

Gwamnan ya tunatar da cewa iyalai da yawa ne suka ci gajiyar N5,000 da aka raba a baya a matsayin tallafi, yana mai cewa matakin na yanzu ya yi daidai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262