“Yan Najeriya Za Su Taka Rawa Da Tsalle a Titi Idan Aka Soke Zaben Tinubu”, PDP

“Yan Najeriya Za Su Taka Rawa Da Tsalle a Titi Idan Aka Soke Zaben Tinubu”, PDP

  • Jam'iyyar PDP ta yi hasashen makomar shugaban kasa Bola Tinubu a kotun zabe
  • Gabannin yanke hukuncin kotun, PDP ta bayyana cewa yan Najeriya za su yi rawan murna idan kotu ta soke nasarar Tinubu a zaben shugaban kasa na 15 ga watan Fabrairu
  • Pedro Obaseki, daraktan dabaru da bincike na kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na PDP, shine ya yi wannan hasashen a wata sanarwa a ranar Laraba, 19 ga watan Yuli

Jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) mai adawa ta bayyana abun da zai faru idan kotun zaben shugaban kasa ta soke nasarar zaben jam'iyyar All Progressives Congress (APC) na ranar 25 ga watan Fabrairu.

Abun da yan Najeriya za su yi idan kotu ta tsige Tinubu, PDP ta bayyana

Jam'iyyar PDP ta bayyana cewa yan Najeriya za su fita tituna don murna idan kotu ta soke nasarar shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a zaben 2023.

Kara karanta wannan

Shugaban APC Na Kasa Adamu Abdullahi Ya Yi Murabus Ne? Ga Abin Da Muka Sani

PDP tace yan Najeriya za su yi murna idan kotu ta tsige Shugaban kasa Bola Tinubu
“Yan Najeriya Za Su Taka Rawa Da Tsalle a Titi Idan Aka Soke Zaben Tinubu” - PDP Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Daily Trust ta rahoto cewa Pedro Obaseki, daraktan dabaru da bincike na kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na PDP, shine ya yi wannan hasashen a Abuja a ranar Laraba, 19 ga watan Yuli.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Nasarar Tinubu: PDP ta nuna karfin gwiwa a kan bangaren shari'a gabannin hukuncin karshe da kotun zabe za ta yanke

Obaseki, wanda ya yi jawabi ga manema labarai gabannin hukuncin kotun zabe, ya kuma nuna karfin gwiwar cewa PDP ta yi amanna da bangaren shari'a na yanke hukunci na gaskiya wanda bangarorin da abun ya zaba za su yarda da shi, jaridar The Guardian ta rahoto.

Ya kuma ce saboda nauyin hujjar da suke da shi, alkalan kotun zaben za su samu karfin gwiwar magance matsalolin da suka taso, inda ya ce martabar kasar na cikin hadari, a cewarsa alkalan ba za su yi wasa da haka ba.

Kara karanta wannan

Shugaban Kasa Tinubu Zai Bar Najeriya Zuwa Kasar Kenya Don Halartan Taron AU

Tinubu na shirin daura Ambode a kujerar sanatan Lagas

A wani labari na daban, mun ji cewa shugaban kasa Bola Tinubu yana duba yiwuwar dawowa da tsohon gwamnan jihar Lagas, Akinwunmi Ambode, a harkokin siyasa.

Majiyoyi da ke da masaniya kan ci gaban sun bayyana cewa shugaban kasar na duba yiwuwar ganin tsohon gwamnan ya zama sanatan Lagas ta gabas yayin da za a yi wa wanda ke rike da mukamin a yanzu, Tokubo Abiru, dannar kirji da mukamin minista.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng