Hukumar INEC Ta Gaza Kare Nasarar Gwamnan PDP a Gaban Kotun Zabe

Hukumar INEC Ta Gaza Kare Nasarar Gwamnan PDP a Gaban Kotun Zabe

  • Hukumar INEC ta gaza gabatar da shaidu domin kare kanta da tabbatar da nasarar gwamnan Enugu na PDP a zaben 2023
  • A ci gaba da zaman Kotun zaɓe ranar Laraba, Lauyan INEC ya ce hukumar ta yi mazari kuma ta fasa gabatar da shaidu
  • A halin yanzu Kotun ta ɗaga zaman da awa 2 domin PDP ta shirya fara gabatar da shaidu da misalin ƙarfe 11:00 na safe

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Enugu state - Hukumar zaɓe ta kasa mai zaman kanta (INEC) ta gaza kare nasarar gwamnan jihar Enugu, Peter Mbah, na jam'iyyar PDP a gaban kotun zaɓe.

Rahoton The Nation ya nuna cewa INEC ta gaza kare tuhumar da ɗan takarar gwamna na Labour Party, Chijioke Edeoga, ya yi a Kotu cewa an tafka magudi a zaɓen gwamnan Enugu 2023.

Kara karanta wannan

"Matata Tana Zabga Mun Mari Ta Lakaɗa Mun Duka Kamar Jaki" Ɗan Kasuwa Ya Nemi Saki a Kotu

Gwamna Peter Mbah na jihar Enugu yana kaɗa kuri'a.
Hukumar INEC Ta Gaza Kare Nasarar Gwamnan PDP a Gaban Kotun Zabe Hoto: Peter Mbah
Asali: Twitter

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan ta ci gaba da zama domin bai wa hukumar INEC damar gabatar shaidunta da zasu gamsar da sahihancin zaɓen da ya ba Peter Mbah nasara.

Sai dai lokacin da aka dawo zaman sauraron ƙarar, INEC ta hannun tawagar lauyoyinta karkashin Humphrey Okoli ta faɗa wa Kotu cewa ta fasa kiran shaidu.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Okoli ya ce:

"Wanda ake tuhuma ta farko watau INEC ce zata kare kanta a halin yanzu, amma bayan nazari kan Kes din hukumar ta yanke shawarar ba zata gabatar da ko shaida ɗaya ba."

Wane mataki jam'iyyar PDP ta ɗauƙa kan haka?

A bangarensa, lauyan PDP, Benjamin Nwosu, da kuma lauyan gwamna Mbah ba su yi musu da matakin INEC ba. Ana tsammanin PDP zata fara kare kanta nan ba da jima wa ba.

Kara karanta wannan

Kano: Ganduje Ya Magantu Kan Batun Ciyo Bashin Biliyan 10 Don CCTV, Ya Fayyace Gaskiyar Al'amari

Jam'iyyar PDP ta nuna cewa ta shirya tsaf zata gabatar da shaidu domin tabbatar da sahihancin sakamakon zaben gwamna, wanda ta lashe a 2023.

PDP ta nemi ƙarin lokaci

Sai dai a halin yanzu jam'iyyar ta gaya wa Kotun sauraron ƙarar zaben cewa tana buƙatar karin lokaci domin samun damar gabatar da kwararan shaidun da ta tanada.

A rahoton Daily Post, Lauyan PDP ya ce:

"Mun shirya fara kare kanmu yau. A yanzu muna rokon Kotu ta ƙara mana awanni biyu gabanin fara gabatar da shaidun mu."

Bayan wannan roko kuma lauyan Edeoga bai yi musu ba, Kotu ta ɗaga zaman da awanni 2, PDP zata fara gabatar da shaidunta da ƙarfe 11:00 na safiyar yau Laraba.

Shema da Tawagarsa Sun Ziyarci Gwamna Dikko Radda a Katsina

A wani rahoton na daban Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗda ya karɓi bakuncin tsohon gwamna, Ibrahim Shema a gidan gwamnatinsa.

Kara karanta wannan

An Yi Son Kai: Majalisa Za Ta Binciki Duka Mukaman da Aka Bada a Mulkin Buhari

Gwamna Radda ya gode wa Shema bisa gudummuwar da ya bai wa APC har ta samu nasarar lashe zaɓe ranar 18 ga watan Maris.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262