“Ya Dauki Hanyar Adams”: Shehu Sani Ya Yi Martani a Kan Murabus Din Adamu

“Ya Dauki Hanyar Adams”: Shehu Sani Ya Yi Martani a Kan Murabus Din Adamu

  • Sanata Shehu Sani ya yi martani a kan murabus din Sanata Abdullahi Adamu a matsayin shugaban jam'iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa
  • Tsohon dan majalisar ya lissafa muhimman abubuwa biyu da suka yi sanadiyar ficewar tsohon gwamnan na jihar Nasarawa
  • Sani ya ambaci ambaci lokacin da Adamu ya ayyana Lawan a matsayin dan takarar maslaha na APC da kuma rashin masaniya a kan jerin sunayen shugabannin majalisa

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Tsohon sanata Shehu Sani, wanda ya wakilci Kaduna ta tsakiya a majalisar dokokin tarayya ta 8, ya lissafa wasu manyan laifuka biyu da suka yi sanadiyar murabus din Sanata Abdullahi Adamu a matsayin shugaban jam'iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa.

Sani ya ce abu na farko shine lokacin da Adamu ya sanar da tsohon shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan a matsayin dan takarar maslaha na APC amma tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar shi a tsaka mai wuya kafin babban taron jam'iyyar na kasa a 2022.

Kara karanta wannan

Shehu Sani Ya Bayyana Yadda Na Hannun Daman Buhari Suka Tsinci Kansu A APC Bayan Zuwan Tinubu

Shehu Sani ya yi martani kan murabus din Abdullahi Adamu daga shugabancin APC
“Ya Dauki Hanyar Adams”: Shehu Sani Ya Yi Martani a Kan Murabus Din Adamu Hoto: Shehu Sani/ Sen. Abdullahi Adamu-APC National Chairman
Asali: Facebook

Ya ce abu na biyu shine Adamu bai da masaniya a kan jerin sunayen shugabannin majalisar dokoki na 10 da aka amince da su.

Ya bayyana hakan ne a wata wallafa da ya yi a shafinsa na Twitter mai suna @ShehuSani a ranar Litinin, 17 ga watan Yuli, yana mai cewa wadannan abubuwa guda biyu sun nuna cewa Adamu na cikin yanayi mai wuyar sha'ani.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

"Daga lokacin da ya sanar da Lawan a matsayin dan takarar maslaha na jam'iyyar mai mulki sannan Buhari ya bar shi a tsaka mai wuya, zuwa lokacin da aka bar shi a cikin duhu kan jerin sunayen manyan jami'an majalisar dokoki na kasa da aka aminta da su, na san cewa Adamu zai bi hanyar Adams."

Shugaban jam'iyya na kasa: An shawarci APC da ta nada Abdullahi Ganduje a kan kujerar Abdullahi Adamu

Kara karanta wannan

Kura-Kurai, Katobara da Cikas 7 da Abdullahi Adamu Ya Samu a Kujerar Shugabancin APC

A wani labarin kuma, mun ji cewa wasu sun fara yin kira ga jam’iyyar APC mai mulki ta nada Abdullahi Umar Ganduje ya zama sabon shugaba na kasa.

Legit.ng Hausa ta bibiyi shafukan sada zumunta, ta gano akwai masu wannan ra’ayi. Wadanda su ke ganin Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya dace ya maye gurbin Abdullahi Adamu, sun yaba da yadda yake kaunar APC.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng