Buhari: Shugabancin Najeriya Na Daya Daga Cikin Kalubale Mafi Tsanani A Rayuwa

Buhari: Shugabancin Najeriya Na Daya Daga Cikin Kalubale Mafi Tsanani A Rayuwa

  • Tsohon shugaban Najeriya, Manjo Janar Muhammadu Buhari, ya bayyana cewa shugabanci a Najeriya cike yake da kalubale mai yawa
  • Buharin ya bayyana hakan ne a cikin wani sako na barka da sallar Eid-el-Kabir da ya aikewa 'yan Najeriya
  • Hakan na zuwa ne a kasa da sa'o'i 24 da Buhari ya yi jawabi kan abinda ya hana shi cire tallafin man fetur

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana shugabancin Najeriya a matsayin daya daga cikin kalubale mafi tsanani a rayuwa.

Tsohon shugaban kasar ya bayyana hakan ne a cikin sakonsa na taya murnar babbar sallah, wato Eid-el-Kabir ga ‘yan Najeriya, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Buhari ya mika ragamar mulki ga shugaban kasa Bola Tinubu a ranar 29 ga watan Mayun 2023, wanda daga nan ne ya koma gefe yana rayuwarsa shi kadai.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu Za Ta Samar Da Ayyuka Miliyan 1 Ga Matasan Najeriya, Kashim Shettima Ya Yi Bayani

Buhari ya ce akwai kalubale a mulkin Najeriya
Buhari ya ce shugabancin Najeriya ne abu mafi tsananin kalubale a rayuwarsa. Hoto: @GarShehu
Asali: Twitter

Buhari ya yi kira ga 'yan Najeriya su ba Tinubu goyon baya

A cikin sanarwar, wacce Mallam Garba Shehu, tsohon mai magana da yawun tsohon shugaban kasar ya fitar a ranar Talata, Buhari ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su goyawa magajinsa baya.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

A cewar sanarwar:

“Jagoranci kasa kamar Najeriya na daya daga cikin kalubale mafi wahala a rayuwa kuma ya bukaci ‘yan Najeriya da su bai wa gwamnatin Tinubu cikakken goyon baya don samun nasara, saboda shugabanci aiki ne mai cike da kalubale da ke bukatar sadaukarwa da goyon bayan ‘yan kasa.”

Buhari ya bayyana dalilin da ya hana ya cire tallafin man fetur

Buhari ya fadi hakan ne cikin abinda bai wuce sa’o’i 24 da ya yi ikirarin cewa, Tinubu zai fadi zabe in a ce ya cire tallafin man fetur.

Kara karanta wannan

Bola Tinubu Zai Dawo Najeriya Yau, Akwai Yiwuwar a Nada Ministoci Bayan Sallah

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin din da ta gabata, Buhari ya kare matakin da ya dauka na kin cire tallafin man fetur a lokacin da yake kan mulki.

Ya bayyan cewa bai cire tallafin ba ne domin gudun kada jam’iyyar APC ta fadi zaben 25 ga watan Fabrairu da ya gabata.

Shehu ya ce akwai tallafi da dama da gwamnatin Buhari ta gada a shekarar 2015, amma duka ya ciresu kafin ya sauka mulki.

Ya ce akwai tallafe-tallafe irin na man dizal, na man jirgin sama, kalanzir, gas din girki da sauransu, wadanda Buhari ya gada amma ya cire su kafin ya sauka mulki.

Sai dai dama tun a lokacin da yake kan madafun iko, tsohon shugaban kasar, ya taba bayyana cewa ba za a iya ci gaba da biyan kudaden tallafin man fetur ba daga 2023.

Kara karanta wannan

NSA: Sabon Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara Kan Tsaron Kasa Ya Kama Aiki Gadan-Gadan

GwamnatinTinubu za ta samar da ayyukan yi miliyan 1 ga 'yan Najeriya

Legit.ng ta kawo muku rahoto a baya da yake cewa, gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, za ta samar da ayyukan yi akalla miliyan daya ga matsan Najeriya.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ne ya bayyana hakan a yayin wani taro da wakilan shugaban Kasar Koriya ta Kudu a Abuja.

Asali: Legit.ng

Authors:
Deen Dabai avatar

Deen Dabai Zaharaddeen Hamisu marubuci kuma ma'aikacin jarida ne da ke da gogewa wajen iya tantance sahihan labarai da na karya. Ya yi digirinsa a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Baya ga haka, ya shafe sama da shekaru 5 a bangaren aikin watsa labarai wanda hakan ya bashi gogewa ta musamman a aikin jarida. Za a iya tuntubarsa ta adireshinsa na yanar gizo: deen.dabai@corp.legit.ng