Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Magana Kan Jerin Sunayen Ministocin Tinubu

Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Magana Kan Jerin Sunayen Ministocin Tinubu

  • Masu fatan ganin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya fitar da sunayen ministocinsa cikin yan kwanakin nan za su yi hakuri su cigaba da jira
  • Hakan na zuwa ne bayan mai magana da yawun Shugaban kasar Dele Alake ya fada wa yan jarida a Abuja cewa hasashen da ake ni game da fitar da ministocin yan kwanakin nan ba gaskiya bane
  • Ya ce kawo yanzu Shugaban kasar bai tattara sunayen wadanda zai nada minista ba amma idan an yi hakan zai sanar da al'ummar kasar

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

FCT Abuja - A karshe fadar shugaban kasa ta yi martani kan hasashen da ake ta yi gamen na cewa an gama tattara sunayen ministocin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Da ya ke martani kan wannan hasashen, Dele Alake, mai magana da yawun shugaban kasa Tinubu, ya ce ba a tattara jerin sunayen ba.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu Ya Shafe Harajin da Aka Lafta, Ya Ƙirƙiro Dokokin Rage Raɗaɗi

Tinubu bai shirya fitar da sunayen ministocinsa ba, Fadar Shugaban Kasa
A cikin kwana 30 na farko kan mulki, Shugaba Tinubu ya yi nade-nade da dama. Hoto: @AsiwajuOladimej
Asali: Twitter

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Mai magana da yawun shugaban kasar ya yi wannan ikirarin ne a ranar Alhamis 6 ga watan Yuli a Abuja yayin da ya ke yi wa manema labarai jawabi.

Abin da Dele Alake ya bayyana game da sunayen ministocin Tinubu

Kamar yadda Premium Times ta rahoto, ya ce:

"Babu alamar gaskiya cikin wadannan abubuwan," Mista Alake ya ce game da jita-jita kan sunayen ministoci.
"Idan Shugaban kasar ya shirya kuma ya natsu, kune na farko da za ku san abin da ya ke son yi."

Dakaci karin bayani ...

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164