Tashin Hankali a Gidan Gwamnatin Jihar Ondo Yayin Da Mataimakin Gwamna Ya Huro Wuta Sai An Mika Masa Mulki

Tashin Hankali a Gidan Gwamnatin Jihar Ondo Yayin Da Mataimakin Gwamna Ya Huro Wuta Sai An Mika Masa Mulki

  • Lucky Orimisan Aiyedatiwa, mataimakin gwamnan jihar Ondo, ya taso gwamnan jihar Rotimi Akeredolu a gaba saboda rashin lafiyarsa
  • Ana zargin Aiyedatiwa da ƙokarin tilasta gwamna Akeredolu, wanda baya da lafiya, ya miƙa masa mulki sannan ya yi murabus
  • Ana kuma zargin mataimakin gwamnan na jihar Ondo da ƴada labarai kan mutuwar gwamnan satin da ya gabata

Akure, jihar Ondo - Akwai ƴar tsama a gidan gwamnatin jihar Ondo yayin da mataimakin gwamnan jihar, Lucky Orimisan Aiyedatiwa, yake son gwamna Rotimi Akeredolu ya miƙa masa mulki ba tare da ɓata lokaci ba.

A cewar wani rahoto da jaridar Vanguard ta fitar ranar Litinin, 12 ga watan Yuni, Aiyedatiwa shi ne ya kitsa jita-jitar da aka yi ta yaɗawa satin da ya gabata kan rashin lafiyar gwamnan da ta mutuwarsa.

Kara karanta wannan

Ashsha: Matawalle Ya Bayyana Irin Satar Da Gwamnatin Zamfara Ta Yi Masa a Gida Da Sunan Kwacen Motoci

Mataimakin gwamnan Ondo na son karbar mulki
Dangantaka ta yi tsami tsakanin Akeredolu da mataimakinsa Aiyedatiwa Hoto: Lucky Aiyedatiwa
Asali: Facebook

Akeredolu yana sane da ƙulla-ƙullar da mstaimakin gwamnan yake yi

Aiyedatiwa ya kitsa jita-jitar ne domin mutanen jihar su goya masa baya ya samu abinda yake so.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Majiyoyi daga cikin gidan gwamnatin jihar sun bayyana cewa Akeredolu yana sane da burin mataimakin nasa na karɓar mulki, a cewar Vanguard.

Majiyoyin sun bayyana cewa:

"Rikicin ya fara ne lokacin da gwamna Akeredolu ya tafi hutun shaƙatawa ya miƙa ragamar mulkin jihar a hannun mataimakin gwamna."
"A ɗan zaman da ya yi a matsayin gwamnan jihar, ana zargin mataimakin gwamnan da fifita son zuciyarsa akan abinda yakamata ya aiwatar a jihar."
"Wasu daga cikin ƴan majalisar zartaswar jihar sun yi zargin cewa mataimakin gwamnan ne yake da hannu akan yaɗa labaran jita-jita kan rashin lafiyar gwamnan."

A satin da ya gabata ne dai rahotannin jita-jita suka yi ta yawo kan mutuwar gwamna Akeredolu, wanda har sai da gwamnatin jihar ta fito ta musanta jita-jitar mutuwar gwamnan.

Kara karanta wannan

Wike Ya Yi Magana Mai Jan Hankali Kan Matakin da Shugaba Tinubu Ya Ɗauka Na Dakatar da Gwamnan CBN

Gwamnan Katsina Ya Soke Filayen Da Gwamnatin Magabacinsa Ta Raba

A wani labarin na daban kuma, gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda ya soke filayen da gwamnatin magabacinsa ta Aminu Bello Masari ta raba a jihar.

Gwamnan ya yi wannan hukuncin ne biyo bayan yadda aka raba filayen ba bisa ƙa'idar doka ba a tsakanin wasu shugabannin ma'aikatu a jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng