Uwar Gidan Shugaban Kasa, Remi Tinubu, Ta Shiga Ofis, Ta Fara Aiki

Uwar Gidan Shugaban Kasa, Remi Tinubu, Ta Shiga Ofis, Ta Fara Aiki

  • Matar shugaban ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta fara shiga ofishin 'First Lady' jiya Litinin, 5 ga watan Yuni, 2023
  • Misis Tinubu, ta ziyarci manyan ofisoshin sashinta domin ganin yadda komai ke tafiya tare da babban sakataren gidan gwamnati
  • A ranar 29 ga watan Mayu, aka rantsar da mijinta, Bola Ahmed Tinubu a matsayin shugaban Najeriya

FCT Abuja - Uwar gidan shugaban ƙasa "First Lady," Sanata Oluremi Tinubu, ta shiga ofishinta domin fara aiki a matsayin mace lamba ɗaya a Najeriya ranar Litinin, 5 ga watan Yuni.

Jaridar The Nation ta rahoto cewa Misis Tinubu ta isa bangaren matar shugaban ƙasa bisa rakiyar masu tsaronta a Villa da ke birnin tarayya Abuja.

Oluremi Tinubu.
Uwar Gidan Shugaban Kasa, Remi Tinubu, Ta Shiga Ofis, Ta Fara Aiki Hoto: Sen. Oluremi Tinubu
Asali: Facebook

Daga zuwanta, ta samu kyakkyawar tarba daga babban Sakataren fadar shugaban ƙasa, Mista Tijjani Umar, da shugabannin ɓangarorin sashin matar shugaban ƙasa.

Kara karanta wannan

Cire Tallafi: Dalilai 5 Da Yasa Yajin Aikin NLC Kan Man Fetur Ba Zai Yi Nasara Ba

Wane aiki matar shugaba Tinubu ta fara yi a ranar farko?

Daga nan, matar shugaban ƙasa ta fara tafiya rangadi domin duba ofishin da ke ɓangarenta, wanda ya haɗa da ofishin shugabanci, ICT, shirye-shirye, midiya da kuma ofishin tsara ayyuka.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

An haifi Oluremi Tinubu a ranar 21 ga watan Satumba, 1960, mahaifiyarta yar kabilar Itsekiri ce yayin da mahaifinta ya kasance bayerabe.

Ta yi aiki a matsayin matar gwamnan jihar Legas tsakanin 1999 zuwa 2007, daga nan kuma ta lashe zaɓen Sanata mai wakiltar Legas ta tsakiya a majalisar dattawan Najeriya.

Sanata Oluremi Tinubu ta shiga harkokin taimako da ba da tallafi da dama da nufin sanya walwala da jin daɗi a fuskokin mutane masu ƙaramin karfi a mazaɓarta.

Ta taɓa haɗa gasar karanto haruffan kalma da aka fi sani da, "Spelling Bee competition," a tsakanin daliban sakandiren jihar Legas wanda ya samar da gwamnan rana ɗaya a zangon mulkin mijinta.

Kara karanta wannan

Abin Da Buhari Ya Gaza Yi A Shekarunsa 8 Kan Mulki, Mataimakin Shugaban APC Ya Yi Bayani

Mai gidanta, Bola Ahmed Tinubu, ya samu nasarar lashe zaben shugaban ƙasa wanda ya gudana a watan Fabrairu kuma aka rantsar da shi ranar 29 ga watan Mayu, 2023.

Shugaba Tinubu Ya Shiga Ganawa da Wike, Umahi da Akpabio a Villa

A wani labarin kuma Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya gana da tsoffin gwamnoni 3 a fadarsa da ke birnin Abuja.

Rahoto ya nuna tsohon gwamnan Ribas, Nyesom Wike, tsohon gwamnan Ebonyi, Dave Umahi da Godswill Akpabio sun isa Villa da karfe 2:33 na ranar Litinin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel