Zaben Gwamnan Kogi: Hotuna Sun Bayyana Yayin da Buhari Ya Lamuncewa Ododo

Zaben Gwamnan Kogi: Hotuna Sun Bayyana Yayin da Buhari Ya Lamuncewa Ododo

  • Dan takarar gwamnan jam'iyyar All Progressive Congress (APC) a jihar Kogi state, Usman Ododo, ya samu yardar shugaban kasa Muhammadu Buhari
  • Gwamna Yahaya Bello ya gabatar da Ododo ga shugaban kasar a fadar Villa a ranar Juma'a, 28 ga watan Afrilu
  • Shugaba Buhari ya bukaci Ododo da ya mayar da hankali kan batutuwa masu muhimmanci yayin yakin neman zabe

FCT Abuja - Gabannin zaben gwamna a jihar Kogi, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya lamuncewa dan takarar jam'iyyar All Progressive Congress (APC), Usman Ododo.

Jaridar The Nation ta rahoto cewar gwamna mai ci, Yahaya Bello ne ya gabatar da Ododo a gaban Shugaban kasa Buhari a fadar shugaban kasa da ke Abuja a ranar Juma'a, 28 ga watan Afrilu.

Dan takarar gwamnan APC a Kogi, Usman Ododo, Shugaban kasa Buhari da Gwamna Yahaya Bello
Zaben Gwamnan Kogi: Hotuna Sun Bayyana Yayin da Buhari Ya Lamuncewa Ododo Hoto: @BashirAhmaad
Asali: Twitter

Jim kadan bayan gabatar da shi, Ododo ya sanar da manema labarai na fadar shugaban kasa cewa ya yi niya kuma a shirye yake ya ci gaba daga inda Gwamna Bello ya tsaya a jihar Kogi idan ya lashe zaben.

Kara karanta wannan

Yanzu Yanzu: Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin PDP 2 a Abuja, Cikakken Bayani Ya Bayyana

Ododo ya bayyana cewa gogewarsa a fannin tattalin arziki a ma’aikatun gwamnati da masu zaman kansu yasa ya dace da jan ragamar shugabanci a jihar Kogi.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Sai dai kuma, ya bayyana cewa yana da tabbacin cewa zai yi nasara a zaben gwamnan da za a yi a ranar 11 ga watan Nuwamba.

Gwamna Yahaya Bello ya ba mazauna Kogi tabbacin ci gaba da Ododo

A daya bangaren, Gwamna Bello ya bukaci mutanen Kogi cewa shugabancin Ododo zai kai jihar ga matakin nasara domin za a ci gaba da ababen more rayuwa a jihar.

Ya ci gaba da cewar jam’iyyar APC reshen jihar Kogi tana nan a hade kuma ta shirya yin nasara zaben gwamnan.

An tattaro cewa yayin zantawa da Shugaba Buhari, an shawarci Ododo da ya bayar da hankali kan muhimman batutuwa yayin yakin neman zabe sannan ya tabbatar da ganin cewa jam’iyyar ta ci gaba da rike kujerarta a jihar, Vanguard ta rahoto.

Kara karanta wannan

Shugaba Buhari Ya Karbi Bakuncin Zababben Shugaban Kasa Tinubu, Hotuna Sun Bayyana

Ododo ya zama dan takarar gwamnan APC a Kogi bayan kammala zaben fidda gwanin jam’iyyar a ranar Juma’a, 14 ga watan Afrilu sannan aka tabbatar da shi a wani taron jam’iyyar na musamman a ranar Asabar, 15 ga watan Afrilu.

Kwamitin karbar mulkin Kano ya zargi Ganduje da yi ma shirin mika mulki zagon kasa

A wani labari na daban, kwamitin karbar mulki na Abba Kabir Yusuf ya zargi Gwamna Abdullahi Ganduje da yi wa shirin mika mulkin jihar zagon kasa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng