Jam'iyyar APC Ta Miƙa Sunayen Yan Takarar Gwamna a Jihohi 3 Ga INEC

Jam'iyyar APC Ta Miƙa Sunayen Yan Takarar Gwamna a Jihohi 3 Ga INEC

  • APC ta tura sunayen yan takarar da ta baiwa tikitin takarar gwamna a jihohin Imo, Bayelsa da Kogi
  • Wannan na zuwa ne bayan jam'iyyar ta kammala zaben fidda gwani a jihohin guda uku
  • Ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023 hukumar zaɓe zata gudanar da zaben gwamna a jihohin

Abuja - Jam'iyyar All Progressives Congress (APC) ta tura sunayen 'yan takararta na gwamna a jihohin Imo, Bayelsa da Kogi zuwa ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC).

Wannan na ƙunshe ne a wata takarda da gwamnan jihar Kogi, Alhaji Yahaya Bello, ya wallafa a shafinsa na dandalin sada zumunta watau TuwitaK da yammacin ranar Lahadi.

Jam'iyar APC.
Jam'iyyar APC Ta Miƙa Sunayen Yan Takarar Gwamna a Jihohi 3 Ga INEC Hoto: @OfficialGYBKogi
Asali: Twitter

Takardan mai ɗauke da adireshin shugaban INEC na ƙasa, Farfesa Mahmud Yakubu, na ƙunshe da sunayen 'yan takarar gwamna a dukkan jihohin uku.

Kara karanta wannan

Jam'iyyar APC Ta Doke Manyan Abokan Karawarta, Ta Lashe Ƙarin Kujerun Yan Majalisa 8

A cewar takardan mai ɗauke da sa hannun muƙaddashin shugaban APC, Sanata Abubakar Kyati da Sakatare, Sanata Iyiola Omisore:

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

"Mun rubuta wannan takarda ne domin aiko da sunayen yan takararmu na gwamna a zaɓen wajen layi dake tafe ga hukumarku"

Jerin 'yan takarar gwamnan APC a jihohin guda uku

A cikin wasiƙar, jam'iyyar APC ta bayyana sunayen mutanen da ta baiwa tikitin takarar gwamna a zaɓen Imo, Bayelsa da Kogi mai zuwa, ga su kamar haka;

1. Mai girma tsohon ƙaramin ministan albarkatun man Fetur, Temipre Sylva - Jihar Bayelsa.

2. Mai girma gwamnan jihar Imo Hope Uzodinma - Jihar Imo

3. Ahmed Ododo - jihar Kogi.

Legit.ng Hausa ta fahimci cewa a ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023, INEC zata gudanar da zabem gwamna a waɗan nan jihohi guda uku.

Kara karanta wannan

Zaben Adamawa: Jam'iyyar PDP Ta Shiga Zanga-Zanga, Ta Sha Wani Muhimmin Alwashi Kan INEC

Gwamna Uzodinma na kokarin zarcewa kan madafun iko a jihar Imo yayin da Ahmed Ododo, wanda ke da goyon bayan gwamna mai ci, ke neman zangon farko a Kogi.

Sylva, tsohon ƙaramin ministan man Fetur na da jan aiki a gabansa, inda zai gwabza da gwamna mai ciki Douye Diri na PDP a yunkurinsa na kwace mulkin Bayelsa.

A wani labarin kuma Jam'iyyar APC Ta Lashe Kujerun Yan Majalisu 8 a Cikon Zaben Jihar Kebbi

Bayan ta lashe kujerar gwamna tun da fari, APC ta ci gaba da samun nasara a jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262