Kotu Ta Mayar Da Tsigaggen Kakakin Majalisar Dokokin Plateau Kan Kujerar Sa

Kotu Ta Mayar Da Tsigaggen Kakakin Majalisar Dokokin Plateau Kan Kujerar Sa

  • Kotu ta mayar da tsigaggen kakakin majalisar dokokin jihar Plateau kan muƙamin sa
  • Kotun ta kuma hana kakakin majalisar dokokin jihar na yanzu kiran kan sa a matsayin shugaban majalisar
  • Tun a cikin shekarar da ta gabata ne dai aka tsige Hon. Nuhu Ayuba Abok a matsayin kakakin majalisar dokokin jihar Plateau

Jihar Plateau- Wata babbar kotun jihar Plateau, a ƙarƙashin jagorancin mai shari'a Nafisa Musa, a ranar Litinin ta mayar da tsigaggen kakakin majalisar dokokin jihar, Hon. Nuhu Abok, a matsayin kakakin majalisar dokokin jihar.

Jaridar Leadership ta rahoto cewa ƴn majalisar dokokin jihar sun tsige Hon. Nuhu Abok ne a ranar 28 ga watan Octoban 2021.

Nuhu Abok
Kotu Ta Mayar Da Tsigaggen Kakakin Majalisar Dokokin Plateau Kan Kujerar Sa Hoto: Bluebrint
Source: UGC

Sai dai, Abok ya garzaya gaban babban kotun jihar domin ƙalubalantar hukuncin ƴan majalisar na tsige shi daga kan muƙamin sa.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Sanya Dokar Kulle a Wani Yanki a Jihar

A cikin hukuncin ta kotun ta tabbatar shaidun da masu shigar da ƙara suka gabatar inda tace ba a tsige ɗan majalisar bisa ƙa'ida ba, a dalilin hakan ta soke tsigewar da aka yi masa.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Kotun ta kuma umurci waɗanda ake ƙara ɗa su bayar N1.5m kuɗin zuwa kotu da N138,000 a matsayin kuɗin shigar da ƙarar.

Kotun ta kuma hana kakakin majalisar dokokin jihar na yanzu, kiran kansa a matsayin shugaban majalisar dokokin jihar. Rahoton Ait Live

Idan ba a manta ba dai, bayan an tsige Abok daga kan muƙamin sa, Hon. Yakubu Sanda, ya maye gurbin sa a matsayin kakakin majalisar dokokin jihar.

Sai dai, Hon. Sanda ya sha kashi a hannun ƴar takarar jam'iyyar People’s Democratic Party (PDP), Hon. Mrs. Happiness Matthew Akawu, a mazaɓar Pengana, a zaɓen majalisar dokokin jihar dana gwamna da aka kammala kwanan nan.

Gwamna Wike Ya Bukaci 'Yan Adawar Jihar Rivers Su Marawa Zababben Gwamnan Jihar Baya

A wani labarin na daban kuma, gwamnan jihar Rivers ya aike da muhimmin saƙo zuwa ga ƴan adawar da suka sha kashi a zaɓen gwamnan jihar.

Gwamna Nyesom Wike ya nemi ƴan adawar da su zo a haɗa kai da su domin ciyar da jihar ta Rivers gaba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng