Rikicin PDP: Dalilin Da Ka Iya Sa Atiku Ya Rasa Kuri’un Kano a Zaben 2023

Rikicin PDP: Dalilin Da Ka Iya Sa Atiku Ya Rasa Kuri’un Kano a Zaben 2023

  • Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP na iya rasa damar kawo jihar Kano a zaben 2023
  • Bayyanar Muhammed Sani Abacha, wanda Atiku da kwamitin NWC na PDP basa so a matsayin dan takarar gwamnan jam'iyyar a jihar babban barazana ce ga takarar Atiku
  • Wata babbar kotun tarayya a Kano ta ayyana Abacha a matsayin sahihin dan takarar PDP a zaben gwamnan 2023 a jihar

Kano - Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Atiku Abubakar na iya rasa kuri'u masu yawa a Kano a babban zaben 2023.

Jihar Kano na daya daga cikin wurare masu yawan kuri'u a Najeriya da suka samar da kuri'u fiye da miliyan 2 cikin masu zabe miliyan 5 da ke da rijista a yayin zaben 2019.

Atiku Abubakar
Rikicin PDP: Dalilin Da Ka Iya Sa Atiku Ya Rasa Kuri’un Kano a Zaben 2023 Hoto: Atiku Abubakar
Asali: Twitter

Shin Atiku zai kawo kuri'un Kano a zaben 2023?

Kara karanta wannan

PDP A Kano: Aminu Wali Ya Bayyana Abin Da Zai Yi Bayan Kotu Ta Ba Wa Abacha Nasara

Koda dai Buhari ya kawo jihar a 2019 inda ya samu kuri'u fiye da miliyan 1 cikin kuri'u miliyan 2 zai yi wuya Atiku ya kawo jihar a zaben 2023.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

A ranar Alhamis, 22 ga watan Disamba, wata babbar kotun tarayya a jihar ta ayyana Muhammed Abacha a matsayin sahihin dan takarar gwamna na PDP a Kano, jaridar The Guardian ta rahoto.

Justis A M Liman na kotun ya umurci hukumar zabe na kasa mai zaman kanta (INEC) ta dauki Abacha sannan ta wallafa sunansa a matsayin dan takarar gwamnan PDP a Kano a zaben 2023.

Halin da ake ciki game da Atiku Abubakar, PDP da Muhammed Sani Abacha a zaben 2023

Hukuncin wanda aka zartar ya hana Sadiq Wali daukar kansa a matsayin dan takarar gwamnan PDP a Kano.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Kotu Ta Kori Wali, Ta Tabbatar Da Abacha A Matsayin Dan Takarar Gwamnan Jihar Kano A PDP

Sai dai kuma, Atiku da kwamitin aiki na PDP ya dauki Wali a matsayin dan takarar gwamnan jam'iyyar a Kano.

Wannan ci gaban ya jefa damar da Atiku ke dashi a jihar Kano a zaben 2023 cikin hatsari domin dai bai taba goyon bayan kudirin Abacha ba.

Alkalin ya zartar cewa kuri'un da aka kadawa Abacha a yayin zaben fidda gwanin da tsagin Sagagi ya gudanar a jihar yana bisa doka, rahoton Daily Trust.

PDP ta rasa mambobinta da dama a jihar Plateau

A wani labarin kuma, Umar Mantu, jigon PDP kuma da ga tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Ibrahiim Mantu ya dauya sheka zuwa jam'iyyar APC.

Hakazalika, mambobin PDP 20,000 sun sauya sheka zuwa jam'iyya mai mulki a kananan hukumomin Mangu da Bokkos.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng