Matan Arewa Na Siyar Da Katunan Zabensu Kan N2000, Dattawan Arewa Sun Koka

Matan Arewa Na Siyar Da Katunan Zabensu Kan N2000, Dattawan Arewa Sun Koka

  • Kungiyar dattawan arewa sun zargi wasu yan siyasa da kokarin murkushe kuri'u a yankin arewacin kasar
  • A cewar dattawan arewar, an gudanar da bincike don sanin matakin barnar da ake aikatawa
  • Sun yi kira ga mutanen arewa kan kada su baiwa kowa katunan zabensu duk rintsi duk wuya

Kungiyar dattawan arewa ta koka kan cewa wasu yan siyasa na amfani da damar talaucin da ke addabar mutane a yankin arewa musamman mata wajen siye katunan zabensu.

A cewar dattawan, hakan wani yunkuri ne na murkushe yawan kuri'u a yankin arewacin kasar.

Daraktan labarai na kungiyar dattawan arewa, Dr Hakeem Baba-Ahmed ne ya bayyana hakan a wata hira da Channels Tv.

Katunan zabe
Matan Arewa Na Siyar Da Katunan Zabensu Kan N2000, Dattawan Arewa Sun Koka Hoto: Sahara Reporters
Asali: UGC

Kungiyar ta NEF ta yi ikirarin cewa an tursasa miliyoyin yan arewa musamman mata sakin katunan zabensu kan kudi N2,000, jaridar Vanguard ta rahoto.

Kara karanta wannan

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Sheke Tsohuwa Mai Shekaru 120 tare da Wasu 5

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Ya ce:

"Kungiyar dattawan arewa ta bi wannan al'amari mai cike da damuwa, tana shawartan shugabannin garuruwa da manyan masu ruwa da tsaki kan hatsarin da ke tattare da tauye hakkin yan kasa masu yawan gaske. Mun kuma gudanar da namu binciken, wanda yasa muka fito muka yi wannan gargadi.
"An sanya dubbai koma mai yiwuwa miliyoyin masu zabe a arewa musamman mata sakin katunan zabensu saboda na goro, a yawan lokuta wanda bai fi N2000 ba.
"A wasu lokutan ana fada masu cewa za a dawo masu da katunansu bayan an gama sarrafadu don biyan karin kudi a matsayin na rage radadin talauci. Ba a dawo da kowani katu. Bincikenmu ya nuna cewa wannan yunkuri na rage karfin kuri'un arewa."

Dalilin da yasa mutane ke siyar da kuri'unsu kan N2000

A cewar dattawan, mutanen da ke aikata wannan ta'asa suna yiwa jam'iyyun siyasa daban-daban aiki.

Kara karanta wannan

Da Ɗumi-dumi: An Sake Samun Ibtila'in Fashewa a Babban Birnin Wata Jiha a Najeriya

Kungiyar ta kuma bayyana cewa suna harin garuruwan da suke ganin jam'iyyunsu ko yan takararsu basu da tasiri sosai.

Dattawan arewan sun kuma koka kan halin talauci da ya mamaye arewa, suna masu cewa wannan na daga cikin abubuwan da suka haddasa hakan.

Hakeem Baba-Ahmed: Abun da zai sa na marawa Peter Obi baya

A wani labarin, kakakin kungiyar dattawan arewa, Hakeem Baba-Ahmed yace zai iya goyon bayan takarar Peter Obi idan har su suka fi dacewa don gaje Shugaban kasa Muhammadu Buhari a zaben 2023.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng