Yadda Jonathan ya tuna da Marigayi Yar’adua, shekaru 12 da rasuwarsa a gadon mulki

Yadda Jonathan ya tuna da Marigayi Yar’adua, shekaru 12 da rasuwarsa a gadon mulki

  • Goodluck Ebele Jonathan ya rubuta ta’aziyya na musamman ga Marigayi Umaru Musa Yar’Adua
  • A yau Shugaba Umaru Musa Yar’ Adua yake cika shekara 12 da rasuwa yana kan karagar mulki
  • A cewar Dr. Goodluck Ebele Jonathan, samun wani tamkar tsohon shugaban Najeriyan zai yi wahala

Abuja - Tsohon shugaban Najeriya, Dr. Goodluck Ebele Jonathan ya yabi tsohon mai gidansa, Marigayi Alhaji Umaru Musa Yar’ Adua.

Jaridar Punch ta rahoto Goodluck Ebele Jonathan yana cewa tsohon shugaban na Najeriya jagora ne mai kishin al’ummarsa, maras son kai.

Shekaru 12 kenan da rasuwar Umaru Musa Yar’ Adua, Dr. Jonathan ya ce samun shugaban kasa irin marigayin yana da matukar wahala.

Jonathan ya fitar da wani sakon ta’aziyya na musamman ne da ya yi wa take da ‘President Yar’Adua: 12 years after’ a shafin Facebook.

Kara karanta wannan

‘Dan shekara 47 mai ji da kudi ya saye fam din APC, zai yi takarar Shugaban kasa a 2023

Yar’Adua ya rasu ne a rana irin ta yau a shekarar 2010. Marigayin ne ya karbi mulki a hannun Olusegun Obasanjo, amma ya rasu yana ofis.

Dr. Jonathan da Marigayi Yar’adua
Umaru Musa Yar’ Adua da Goodluck Ebele Jonathan
Asali: Getty Images

‘Shugaba Yar’Adua: Bayan shekaru 12."

“Shekaru 12 da suka wuce, kasarmu ta rasa mai kishi, shugaba maras son kai, mai kawo zaman lafiya, wanda yayi mulki da sha’awa da gaskiya.”
“Shugaban kasa Umaru Musa Yar’ Adua ba ya tare da mu a yau, amma tambarin da ya bari a wajen jagorantar al’umma ya sa ana ta tunawa da shi.”
“Kamar ‘dan wasan da yake tsere cikin nishadi, haka ya yi imani har ya kai karshen tseren. A yau za mu iya cewa ya ciri tuta wajen zaman lafiya.”
“Dakare ne na gaskiya, wanda ya yarda da adalci da tsarin damukaradiyya. Jagora na shi mai bautawa al’umma, kuma mutumin kwarai.”

Kara karanta wannan

Jonathan ya amsa kiran masoyansa, yau za a gabatar da fam din shiga takararsa a APC

- Goodluck Ebele Jonathan

A karshe Jonathan ya kare sakon ta’aziyyarsa da cewa samun irin Marigayin, yana da wahala.

“Ya kasance mai gidana.”
“Shugaba Yar’adua, a yau mu na tuna ka, kuma za mu cigaba da tuna ayyukan kirkin da ka yi wa kasarmu. Ka nuna kishi da hidimar al’umma.”

- Goodluck Ebele Jonathan

Mutuwar Abiola

Kwanan nan aka ji labari cewa Abdul Abiola ya fito yana kira ga Muhammadu Buhari ya binciki mutuwar mahaifinsu da mai dakinsa, Kudirat Abiola.

Cif MKO Abiola wanda ake tunanin zai lashe zaben 1993, ya mutu ne yayin da yake tsare a kurkuku ana tsakar maganar shirin fito da shi a 1998.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng