2023: Bidiyon Ziyarar Da Wike Ya Kai Wa Mahaifiyar Marigayi Ƴar'Adua a Katsina

2023: Bidiyon Ziyarar Da Wike Ya Kai Wa Mahaifiyar Marigayi Ƴar'Adua a Katsina

  • Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike ya kai wa mahaifiyar tsohon shugaban kasa Umaru Musa Yar’Adua, Hajia Aya Dada Yar’Adua ziyara a Katsina
  • Wike yanzu haka dan takarar shugaban kasa ne karkashin jam’iyyar PDP kuma ya kai mata ziyara ne tare da tsohon Gwamna Ibrahim Shema ranar Talata
  • Ya kai ziyarar ne yayin da ake shirye-shiryen yin zaben fidda gwanin jam’iyyar inda ya gaisa da ita da harshen Turanci yayin da Shema ya ke fassara mata

Katsina - Nyesom Wike, Gwamnan Jihar Ribas, ya kai ziyara ga mahaifiyar tsohon shugaban kasa Umaru Musa Yar’Adua, Hajia Aya Dada Yar’Adua a Katsina, Daily Trust ta ruwaito.

Wike dan takarar shugaban kasa ne karkashin jam’iyyar PDP, kuma ya kai ziyara ne a ranar Talata tare da tsohon gwamnan Jihar Katsina, Ibrahim Shema kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Kara karanta wannan

‘Dan shekara 47 mai ji da kudi ya saye fam din APC, zai yi takarar Shugaban kasa a 2023

2023: Wike Ya Kai Wa Mahaifiyar Tsohon Shugaban Kasa Yar'Adua Ziyara a Katsina
2023: Wike Ya Kai Wa Mahaifiyar Kasa Yar'Adua Ziyara a Katsina. Hoto: Daily Trust.
Asali: Twitter

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Yar’Adua ya rasu ne yayin da ya ke kan karagar mulki shekaru 12 da su ka gabata.

Ya kai ziyarar ne yayin da zaben fidda gwanin PDP ya ke karatowa

Wike ya kai ziyarar ne don samun damar ganawa da wakilan jam’iyyar PDP yayin da zaben fidda gwanin jam’iyyar ya ke karatowa kamar yadda Daily Trust ta nuna.

A wani bidiyo na sakwanni 25, an ga Wike ya na gaisawa da mahaifiyar Yar’Adua inda ya yi mata sallama sannan ta amsa.

Mahaifiyar Yar’Adua ta yi godiya ga Gwamnan Ribas din da harshen Hausa inda Shema ya ke fassara ma Wike, bisa ziyarar da ya kai mata.

Ga bidiyon a kasa:

Wike ya gana da Masari

Bayan isarsu gidan Gwamnatin Muhammadu Buhari da ke Katsina, Wike ya je har wurin Masari domin sanar da shi kudirinsa na tsayawa takarar shugaban kasa a 2023 inda ya nemi goyon bayansa.

Kara karanta wannan

Jonathan ya amsa kiran masoyansa, yau za a gabatar da fam din shiga takararsa a APC

Masari ya bukaci duk wasu ‘yan siyasar kasar nan da su kasance masu zage damtse wurin ganin ci gaban kasa idan ba haka ba kowa zai wahala.

Masari ya yaba wa Wike akan babbar rawar da ya taka wurin dakatar da IPOB daga bulla Jihar Ribas, inda ya kara da cewa hakan ya tallafa wa siyasa a Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164