Masu cin gajiyar N-Power sun yi karo-karo, sun tara Miliyoyin Naira zasu siya wa ɗan takara Fom a Kano

Masu cin gajiyar N-Power sun yi karo-karo, sun tara Miliyoyin Naira zasu siya wa ɗan takara Fom a Kano

  • Ma'aikatan tsarin N-Power a jihar Kano sun taimaka wa Sha'aban Sharaɗa da kuɗi miliyan N10m don cimma burinsa a 2023
  • Sharaɗa, ɗan majalisa mai wakilatar mazaɓar Kano Municipal, ya na daga cikin yan takarar gwamnan Kano karkashin APC
  • Wata ƙungiya FJK ta bi sahun masu cin gajiyar shirin, ta tara wa ɗan majalisar wasu miliyan N10m na daban

Kano - Aƙalla yan Najeriya 2,700 dake cin gajiyar tsarin N-Power a jihar Ƙano ne suka yi karo-karon tara kudi miliyan N10m domin goyon bayan takarar gwamnan Sha'aban Sharaɗa, mamba a majalisar wakilan tarayya.

Wannan na zuwa ne bayan wata ƙungiyar ma'aikata duk a jihar Kano wacce ake wa laƙabi da Fitilar Jama’ar Kano (FJK) ta tattara Miliyan N10m domin taimaka wa cikar burinsa na zama gwamna.

Shirin N-Power.
Masu cin gajiyar N-Power sun yi karo-karo, sun tara Miliyoyin Naira ga ɗan takarar gwamnan Kano Hoto: Dailytrust.com
Asali: UGC

Honorabul Sha'aban Sharada, a yanzu haka shi ne ɗan majalisa mai wakiltar Kano Municipal a majalisar wakilan tarayyan Najeriya, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Haka nan kuma Sharaɗa ya na daga yan takarar dake hangen kujerar gwamnan jihar Kano ƙarƙashin inuwar jam'iyyar APC a zaɓen 2023 dake tafe.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Ta ya ma'aikata suka iya haɗa makudan kudi haka?

Da yake miƙa wa ɗan majalisan cakin kudin a madadin sauran ma'aikatan N-Power, shugaban su na jihar Kano, Abba Lawan, ya faɗi yadda suka yi namijin kokari suka haɗa kudin.

A jawabinsa ya ce:

"Kowane ma'aikaci ɗaya daga cikin mu ya ba da gudummuwar Naira Dubu N5,000 ta hanyar aje Dubu Ɗaya a kowane wata na tsawon watanni biyar."

A bangaren sa, yayin da yake karɓan gudummuwar a madadin ɗan majalisan, ɗaya daga cikin shugabannin FJK, Mansur Kurugu, ya ce kungiyarsu ba'a barta a baya ba, ta haɗa miliyan N10m don tallafawa ɗan majalisan.

A wani labarin kuma Fitattun Attajirai biyu sun lale miliyan N200m zasu siyawa mutum biyu Fom ɗin takarar shugaban ƙasa a APC

Wasu yan kasuwa guda biyu yan asalin jihar Abia sun shirya lale makudan kuɗi Miliyan N200m don siya wa mutum biyu Fom a APC.

A wata sanarwa da suka fitar a Abuja , fitattun Attajiran sun ce sun gano kwarewa da salon mulki a jikin Sanata Ahmad Lawan da Orji Kalu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Tags: