Kai Tsaye: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021

All posts
Key Events
Analysis
Exclusive
22 Posts
Sort by
Our live updates have concluded for the day. Catch up on everything you missed below.
Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Za a ci gaba da kada kuri'a a rana ta biyu na zaben gwamnan Anambra

A yau ne za a baiwa masu kada kuri'u da suka cancanta damar kada kuri’unsu a zaben gwamnan jihar Anambra, saboda matsalolin fasaha da gazawar tsarin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta samu.

Sabanin fargabar tashe-tashen hankula a gabanin zaben, an samu fitowar masu kada kuri'a a ko'ina kuma an gudanar da zabe cikin lumana, Vanguard ta ruwaito.

Sai dai malan zabe ba su isa kan lokaci a rumfunan zabe da dama ba, kuma amincewar da INEC ta baiwa masu kada kuri’a ta hanyar tsarin tantance masu kada kuri’a, BVAS, ya fuskanci koma baya a rumfunan zabe da dama a fadin jihar.

Biyo bayan korafin da wasu ‘yan takara da manyan ‘yan siyasa suka yi, INEC ta tsawaita kada kuri’a har zuwa ranar Lahadi.

An kuma tsawaita atisayen fiye da lokacin rufewa da karfe 2:30 na yammacin jiya Asabar.

Kwamishinan zabe na INEC a jihar Anambra, Dokta Nkwachukwu Orji, ya ce BVAS ta gaza a fannoni da dama saboda matsalar manhaja da aka samu.

A cewarsa, saboda haka an kara wa’adin ne domin a baiwa wadanda ba su samu damar kada kuri’unsu yin hakan.

Rukunan zabe da yawa sun fuskanci kutse, wanda hakan ya jinkirta tsarin jefa kuri'a da jin takaicin daga masu jefa kuri'a.

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Sama da mutum 2,500 basu kada kuri'a ba a kauyen Ezinifite Okpuno

A rumfa ta 8 da ke kauyen Ezinifite Okpuno, karamar hukumar Awka ta kudu, sama da mutum 2,500 basu kada kuri'a ba.

Daga cikin mutum 3,072 da suka yi rijista, mutum 150 kacal suka kada kuri'a.

Kai Tsaye: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
Kai Tsaye: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
Source: UGC

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

An fara kirgen kuri'u

An fara kirgen kuri'u a Amawbia Ward 1, PU 10

Kai Tsaye: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
Kai Tsaye: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
Source: UGC

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Hukumar INEC ta kara lokacin kada kuri'a sakamakon matsalar da aka samu da na'urar BVAS

Kwamishanan INEC na jihar Anambra ya sanar da dage lokacin rufe kada kuri'a zuwa karfe 4 na yamma sakamakon matsalolin da aka fuskanta da na'urar BVAS a wurare daban-daban.

Kwamishanan, Dr Nkwachukwu Orji, ya sanar da hakan ne ga manema labarai a hedkwatan INEC dake Awka.

Ya bayyana cewa akwai yiwuwan a cigaba da zaben har zuwa gobe/

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

An yi awon gaba da wani dan sanda wanda ya bugu da giya kafin zuwa rumfar zabe

Bayan jama'a sun yi korafi kan yadda wani jami'in dan sanda wanda ya debi barasa kafin zuwa rumfar zabe keyi, an yi awon gaba da shi.

KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
Source: Original

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Shugabanci nagari muke so, cewar tsohon mai shekaru 70 da aka tantance

Peter Akpati, tsohon mai shekaru 70 ne da aka tantance domin kada kuri'a a rumfar zabe ta 9 da ke gundumar Agu Awka.

A yayin zantawa da Legit.ng, Akpati ya ce: "Jama'a su fito su kada kuri'a, babu amfanin tsoro. Akwai isasshen tsaro.
"Muna bukatar shugabanci nagari a Anambra kuma hakan ne kadai zai taimaka mana wurin zaben wanda muke so."
KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
Source: UGC

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Tsohuwa mai shekaru 70 ta cire tsoro ta fito kada kuri’a

Wata ‘yar shekara 70 mai suna Catherine Egbuche, wacce ta kasance gurguwa ta fito domin kada kuri’a a rumfar zabe ta Amaubia Primary School, Amawbia, jihar Anambra.

Da take zantawa da Legit.ng, Catherine ta ce ta fito domin shiga tsarin zaben duk da cewar har yanzu bata samu kudin sallamarta ba a matsayinta na ‘yar fansho.

KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
Source: Original

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

A karshe Soludo ya isa rumfar zabe

Dan takarar jam'iyyar APGA Charles Soludo ya isa rumfar zabensa don kada kuri'a.

Yanzu kusan karfe 12:30 amma ba mu fara zabe ba," in ji Soludo.

Dan takarar na APGA ya ce zai sake jawabi ga manema labarai bayan ya kada kuri'arsa cikin nasara.

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Dan takarar APC Andy Uba ya kada kuri’a, ya ce babu abun da zai hana shi lashe zabe

Dan takarar jam'iyyar All Progressives Congress (APC) a zaben gwamnan jihar Anambra, Sanata Andy Uba ya kada kuri'arsa.

Legit.ng ta rahoto cewa yayin da yake jawabi bayan kada kuri'a, Uba ya ce an riga an gama zabe yayin da ya nuna yakinin cewa zai lashe zaben.

Ya ce:

"Komai na tafiya daidai. Ta kare ma APGA, babu inda PDP za ta je."
Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Dan takara Ozigbo ya yi jawabi bayan kada kuri'a

Bayan kada kuri'a, dan takarar PDP, Valentine Ozigbo ya ce ya yi matukar farin ciki ganin yawan jama'a da suka fito zaben.

"A gaskiya na ji dadin ganin abinda ke faruwa a yankin Amezi. Na ga masu zaben sun fito sosai," yace.

Ozigbo ya yi korafin cewa an yi jinkiri kafin fara zaben.

"Ban ji dadi da lamarin ya dade ba a fara ba," yace.

Dan takarar PDP ya ce an samu matsalar sabis a yayin da masu kada kuri'a suka taru.

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Jami'an tsaro sun mamaye rumfunan zabe a Awka

Jami'an tsaro sun mamaye rumfunan zabe da ke Akwa, a jihar Anambra

KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
Source: UGC

KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
Source: UGC

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Dan takaran jam'iyyar, Valentine ya dira rumfar zabensa don kada kuri'a

Dan takaran jam'iyyar, Valentine Ozigbo, tare da iyalinsa sun dira rumfar zabensa dake Social Centre, Amesi, karamar hukumar Aguata don kada kuri'arsu.

KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021 Hoto: TVC News
Source: Facebook

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Gwamna Willie Obiano da matarsa sun kada kuri’a

Gwamna Willie Obiano da matarsa, Ebelechukwu sun kada kuri’arsu a rumfar zabe ta Eri Primary school, PU 004, Otuocha 1, Aguleri, karamar hukumar Anambra ta gabas da misalin karfe 9:28 na safe.

Gwamnan wanda ya zanta da manema labarai jin kadan bayan kada kuri’arsa ya ce:

“Na bukaci mutanen Anambra da su fito su yi zabe. Ko ina akwai zaman lafiya. Ku fito ku yi zabe.”
KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021 Hoto: TVC
Source: UGC

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Masu kada kuri'a sun balle zanga-zanga kan dokar INEC ta hana marasa takunkumi zabe

Masu kada kuri'a a gunduma ta 9 da ke Ezimezi a Amawbia, karamar hukumar Awka ta kudu, sun balle zanga-zanga kan dokar INEC ta hana marasa takunkumin fuska saka kuri'a.

Masu zaben sun dinga tururuwar fitowa tun wurin karfe 8:30 amma sai aka ce su koma gida tare da sako takunkumin fuska, Punch ta wallafa.

Wannan lamarin ne yasa tsohon dan majalisar jihar Anambra, Chikodi Aghanya ya kwatanta lamarin da 'shirme'

KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
Source: UGC

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Na'urar BVAS ta mazabar Soludo ba ta aiki

Masu kada kuri'a sun fusata. Kamar yadda suka ce, na'urar BVA ba ta aiki a mazabar dan takarar Charles Soludo.

"Babu abinda ke aiki a nan, ga katin zabe na," wani mai kada kuri'a ya sanar da Arise News TV.

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Mazabar Sanata Andy Uba

Har yanzu jami'an INEC ba su iso mazabar Andy Uba ba, kamar yadda Arise TV ta wallafa

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

An fara kada kuri’a a zaben gwamnan Anambra na 2021

Da misalin karfe 8:30 na safe, an fara kada kuri’a a rumfar zaben PU005, Umudioka, karamar hukumar Dunukofia da rumfar zabe ta Area 13, Ichida 1, karamar hukumar Anaocha.

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Rumfar zabe: Eri Primary school, PU 004

Rumfar zabe: Eri Primary school, PU 004, Otuocha 1, Aguleri, karamar hukumar Anambra ta gabas.

Har zuwa karfe 8:00 na safe, jami’an INEC suna nan suna shirye-shirye, sannan akwai masu jefa kuri’u yan kadan da ke duba sunayensu.

A wannan rumfa ne Gwamna Willie Obiano zai kada kuri’arsa.

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Rumfar zabe: PU001 – Kindergarten Primary School, Obuofu 1

Rumfar zabe: PU001 – Kindergarten Primary School, Obuofu 1, Ward 05, Abagana III, karamar hukumar Njikoka.

A PU001, jami’an INEC na nan suna manna sunayen masu zabe da aka yi wa rijista, da kuma kafa rumfar zabe.

Zuwa yanzu masu jefa kuri’u uku sun hallara. Gaba daya an yi wa mutane 516 rijista, a bisa rahoton The Cable.

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Dan takaran jam'iyyar AAC, Chidozie Nwankwo ya janye daga takarar zaben gwamnan Anambra

Dan takara jam'iyyar jam'iyyar African Action Congress AAC, Chidozie Nwankwo, ya janye daga takarar kujeran gwamnan jihar Anambra.

Nwankwo ya sanar da cewa dukkan wadanda sukayi niyyar zabensa yanzu kawai su goyi bayan dan takaran jam'iyyar PDP, Valentine Ozigbo.

Rahoto BBC

KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021
KAI TSAYE: Yadda ake fafatawa a zaben gwamnan Anambra na 2021 Hoto: BBC Pigdin
Source: Facebook

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

Ba za a yi zabe ba a rumfunan zabe 86, in ji INEC

Yayin da yan Anambra ke shirin zabe, a lura cewa hukumar INEC ta bayyana a baya cewa ba za a yi zabe ba a rumfuna 86 cikin rumfunar zabe 5,720 da ke jihar saboda basu da masu jefa kuri'u.

Aisha Musa avatar Abdul Rahman Rashid avatar Aisha Khalid avatar
daga Aisha Musa, Abdul Rahman Rashid and Aisha Khalid

An yi gyara a tsarin tsaro

Sufeto Janar na yan sandan, IGP Alkali Usman Baba ya cire mataimakin Sufeto Janar na yan sandan, DIG Joseph Egbunike a matsayin shugaban tawagar tsaro na zaben gwamnan Anambra yan sa’o’I kafin zaben.

Kakakin rundunar yan sandan kasar, CP Frank Mba, ya tabbatar da cewar an sauyawa DIG Egbuike wurin aiki, amma bai bayyana dalilin cire babban jami’in wanda ya kasance dan asalin jihar Anambra ba.

Sai dai kuma, kakakin shiyar, Princess Nkeiruka Nwode, ta ce DIG Egbunike bai yi murabus ba kamar yadda aka rahoto a wasu bangarori.