Abin Tsausayi: An Shiga Firgici da Aka Gano Gawarwakin Mutane Sama da 60 a Jihar Neja
- Ana ci gaba da samun bayanai daga mummunan harin da yan bindiga suka kai yankin karamar hukumar Shiroro a Neja ranar Talata da ta wuce
- Rahoto ya nuna cewa zuwa yanzu an gano gawarwakin mutane akalla 61, wadanda suka kunshi jami'an tsaro da fararen hula
- Mazauna yankin da abin ya shafa sun fara barin gidajensu bayan samun rahoton cewa 'yan bindiga na shirin sake kawo hari
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Niger, Nigeria - An gano aƙalla gawarwaki 61 na jami’an tsaro da fararen hula da aka kashe a harin ‘yan bindiga da aka kai ranar Talata a garuruwan Bagna da Erena da ke ƙaramar hukumar Shiroro, jihar Neja.
Mazauna yankin sun ce an kwaso gawarwakin ne a dazukan da ke kusa kwanaki kadan bayan harin yan bindigar, inda aka binne fararen hula a garin Erena.

Source: Original
A rahoton da jaridar Premium Times ta wallafa yau Juma'a, ta ce an kai gawarwakin jami’an tsaro zuwa dakin ajiye gawa na asibitin gwamnati da ke Minna.
An kashe jami'an tsaro da fararen hula
Wani mazaunin Erena wanda ya nemi a sakaya sunansa ya ce:
"Daga cikin waɗanda aka kashe akwai ‘yan banga, jami’an hukumomim tsaro daban-daban da kuma bayin Allah fararen hula
Sai dai rahotanni sun nuna cewa rundunar ‘yan sanda reshen jihar Neja ta tabbatar da mutuwar ‘yan banga uku kacal.
Daya daga cikin waɗanda suka mutu shi ne shugaban ‘yan bangar yankin mai suna, Manga, wanda aka ceto da rai bayan ya ji rauni a artabu, amma daga bisani ya rasu sakamakon raunukan harbin bindiga.
Martanin mazauna yankin
Mazauna yankin sun yaba da kokarin jami’an tsaro da suka kai dauki, inda suka ce daga karshe sun fatattaki ‘yan bindigar.
Sai dai sun zargi gwamnati da gazawa wajen daukar mataki tun da wuri duk da bayanan sirri da aka samu kafin harin.
Bayan harin, fargaba ta karu a yankunan da ke kusa, inda a ranar Alhamis, mazauna yankin Bassa suka fara tserewa daga gidajensu bayan fara jita-jitar cewa za a sake kawo masu hari.

Source: Twitter
Mutane sun fara barin gidajensu
An ga mata da yara suna kokarin tserewa ta cikin kwale-kwale, a daidai lokacin da ake hasashen daruruwan mutane sun rasa matsugunansu a yankin.
Rahoto ya nuna cewa a yanzu suna samun mafaka a makarantar firamare ta Zumba da sauran wurare da suka fi tsaro a Shiroro, kamar yadda Vanguard ta rahoto.
Wani manomi, Rabiu Iliyasu, ya ce:
“Mun ga jiragen sama suna kai hare-hare a kusa da mu. Jami’an tsaro suka janye domin kauce wa kuskure, mu kuma muka gudu saboda babu kariya.”
Shi ma wani mazauni, Suleiman Abdullahi, ya ce jita-jitar taruwar ‘yan bindiga ne ya sa jami’an tsaro suka shawarci mutane su boye ko su fice daga yankin.
Boko Haram ya tarwatsa gada a jihar Neja
An ji cewa 'yan ta'addan Boko Haram sun yi amfani da bam wajen tarwatsa wata gada mai muhimmanci a hanyar Wawa zuwa Guffanti a jihar Neja.

Kara karanta wannan
DSS ta gano tsohon 'dan majalisa da ya kada hantar Amurka da rashin tsaro a Najeriya
Wannan hanya, wadda ta kasance mai cike da hada-hadar mutane da ababen hawa, ta ratsa har ta cikin dajin Kainji Lake National Park.
Mazauna yankin sun bayyana cewa wannan harin da ya tarwatsa gadar ya nuna ƙudurin 'yan ta'addan na durƙusar da tattalin arziƙin jama'ar da ke rayuwa a garuruwan wajen.
Asali: Legit.ng

