‘Ku Kwantar da Hankulanku’: Martanin Najeriya bayan Gargadin Amurka a Abuja
- Gwamnatin tarayya ta yi martani bayan Amurka ta bukaci wasu yan kasarta da su yi gaggawar barin Abuja
- Ministan yada labarai, Mohammed Idris ya bayyana gargadin a matsayin matakin kariya na cikin gida ba matsalar tsaro ba
- Gwamnati ta ce ana samun ci gaba a harkar tsaro ta hanyar ayyukan sojoji da bayanan sirri da ake samu
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bayyana cewa kasar na nan cikin kwanciyar hankali kuma tana aiki yadda ya kamata.
Hakan ya biyo bayan wani gargadi da Amurka ta fitar inda ta bukaci wasu yan kasar da su fice daga birnin Abuja.

Source: Getty Images
Hakan na cikin wata sanarwa da Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya fitar wanda ma'aikatar ta wallafa a Facebook.
Najeriya ta magantu bayan gargadin Amurka a Abuja
A cikin sanarwar, Mohammed Idris ya ce dukkan cibiyoyin gwamnati na ci gaba da aiki yadda ya kamata.
Sai dai gwamnati ta bayyana wannan mataki a matsayin na kariya kawai, bisa tsarin cikin gida na jakadanci, ba wai yana nuni da halin tsaro na kasa baki daya ba.
Ya kara da cewa babu wani cikas ga tafiyar da gwamnati, tattalin arziki, ko rayuwar yau da kullum a fadin kasar.
Ministan ya ce hukumomin tsaro na samun nasarori a ayyukansu ta hanyar hadin gwiwar sojoji, amfani da bayanan sirri, da kuma ingantaccen hadin kai tsakanin hukumomi.
A cewarsa, wadannan kokari sun taimaka wajen dakile ayyukan kungiyoyin masu laifi tare da inganta tsaro a yankuna daban-daban na kasar.
Ya ce:
“Hukumomin tsaro na ci gaba da kokarin kare rayuka da dukiyoyi, kuma ana ganin sakamakon wadannan kokari a zahiri.”

Source: Twitter
Yadda Najeriya ta bude kofa ga kowa
Ministan ya kara da cewa Najeriya na bude ga kasuwanci, yawon bude ido da kuma zuba jari, inda gyare-gyaren tattalin arziki ke kara karfafa amincewar masu zuba jari.

Kara karanta wannan
Bayan hare haren da aka kai a jihohin Arewa, Tinubu ya tunkari matsalar tsaro gadan gadan
Ya bukaci kasashen duniya da abokan hulda su dogara da sahihan bayanai kuma sababbi game da halin tsaro a Najeriya.
Sanarwar ta biyo bayan gargadin tsaro da ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja ya fitar, wanda ya jawo hankalin jama’a da tattaunawar diflomasiyya.
Gwamnatin Najeriya ta jaddada cewa irin wadannan gargadi na kasashen waje ba su canza gaskiyar cewa ana samun ci gaba a harkar tsaro a sassa daban-daban na kasar ba.
Najeriya ta magantu kan yakin Iran da Isra'ila
A wani labarin, an ji cewa ministan yada labarai na kasa, Mohammed Idris, ya ce Najeriya a shirye take ta taimaka wajen magance rikicin makamashi da ke faruwa a duniya.
Ministan ya bayyana hakan ne yayin da yake magana kan rufe mashigar Hormuz da Iran ta yi a rikicin Gabas ta Tsakiya, a wata hira da ya yi.
Kalaman Mohammed Idris sun fara janyo martani iri-iri daga ‘yan Najeriya, inda wasu suka koka cewa har yanzu kasar ba ta iya biyan bukatun cikin gida ba.
Asali: Legit.ng
