Kisan Gilla a Jos Ya Dauki Hankalin Amurka, Dan Majalisa Ya Shawarci Tinubu

Kisan Gilla a Jos Ya Dauki Hankalin Amurka, Dan Majalisa Ya Shawarci Tinubu

  • Dan majalisa daga Amurka, Riley Moore ya yi magana kan harin da aka kai a Jos a ranar Lahadi 29 ga watan Maris, 2026
  • Moore ya soki hare-haren da aka kai wa Kiristoci a Jos, ya bukaci Najeriya ta ƙarfafa tsaro domin kare lafiyar al'ummar kasar
  • Ya gargadi cewa ci gaba da kashe-kashe na iya lalata dangantakar diflomasiyya tsakanin Amurka da Nigeria

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Jos, Plateau - Wani dan majalisar dokokin Amurka, Riley Moore, ya yi kakkausar suka kan hare-haren da ake kai wa Kiristoci a Najeriya.

Moore ya yi gargadin cewa harin da aka kai a Jos na iya janyo matsala a dangantaka tsakanin kasar Amurka da Nigeria ta bangarori da dama.

Dan majalisar Amurka ya yi Allah wadai da harin Plateau
Dan majalisa daga kasar Amurka, Riley Moore. Hoto: @RepRileyMoore.
Source: UGC

Kisan Jos: Martanin dan majalisar Amurka

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, Moore ya bayyana kashe-kashen a matsayin wani abin damuwa, bayan rahoton cewa an kashe akalla Kiristoci 10 a Anguwan Rukuba da ke Jos, a ranar 'Palm Sunday'.

Kara karanta wannan

Yaki da Iran: An kawo dabarar hambarar da Trump daga shugaban kasar Amurka

Ya ce irin wadannan hare-hare sun zama ruwan dare a lokutan bukukuwan addini, yana mai cewa dole ne hukumomin Najeriya su dauki matakai masu tsauri domin dakile zubar da jini a nan gaba.

Moore ya ce:

“A wannan rana ta 'Palm Sunday', rahotanni daga Najeriya sun nuna cewa an kashe akalla Kiristoci 10 a birnin Jos.
‘Yan ta’adda sun bude masu wuta kafin su sare su da adduna, abin takaici ne kuma ba za a amince da shi ba.”
Dan majalisar Amurka ya ba Tinubu shawara kan tsaro
Dan majalisa daga Amurka, Riley Moore da Bola Tinubu na Najeriya. Hoto: @RepRileyMoore, Bayo Onanuga.
Source: Twitter

Shawarar Moore ga gwamnatin Bola Tinubu

Moore ya kara da cewa irin wannan hari yana daga cikin jerin hare-haren da ake kai wa Kiristoci a ranakun bukukuwan addini, yana mai zargin cewa irin wadannan abubuwa na faruwa akai-akai a Najeriya.

Dan majalisar ya bukaci gwamnatin tarayya ta kara tsaurara matakan tsaro kafin bukukuwan 'Triduum da Easter', yana mai gargadin cewa rashin daukar mataki zai iya haifar da mummunan sakamako a dangantakar kasashen biyu.

Ya ce:

“Dole ne gwamnati ta dauki wannan barazana da muhimmanci, ta kuma tashi tsaye wajen kare rayukan Kiristoci, in ba haka ba hakan na iya jawo babbar matsala a dangantakar Najeriya da Amurka.”

Kara karanta wannan

Wata sabuwa: Trump ya fasa kwai, ya bayyana abin da jagororin Iran ke tsoro

Rahotanni sun nuna cewa jihohin yankin Arewa ta Tsakiya da Arewa maso Yamma na fuskantar hare-hare daga ‘yan bindiga da sauran kungiyoyin dauke da makamai a baya-bayan nan.

Ganin dan Amurka ya jawo magana a Plateau

Mun ba ku labarin cewa masu sharhi kan lamuran yau da kullum sun fara magana kan wani dan kasar Amurka, Alex Birbir da ke yawo a kauyukan jihar Plateau.

Rahotanni sun nuna cewa Alex Birbir na shiga kauyuka ne a jihohin Arewa ta Tsakiyan Najeriya da sunan wa'azi da wayar kan Kiristoci musamman kan matsalolin tsaro.

Yawon da Alex Birbir ke yi ya fara daukar hankali ne bayan ganin shi a wajen da aka kai hari aka kashe mutane da dama a cikin dare a birnin Jos da ke jihar Plateau.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.