'Ina Neman Afuwa': Ɗan Nasir El Rufai Ya ba Shettima Hakuri kan Rubutu a Kansa
- Dan tsohon gwamnan Kaduna, Bashir El-Rufai, ya nemi afuwa ga mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima kan kalamansa
- Ya ce sakon nasa kuskure ne kuma wanda dacewa, yana mai jaddada cewa yana girmama Shettima, tare da musanta cewa an tilasta masa janye kalaman
- Lamarin ya zo ne yayin da ake rikicin siyasa da ya shafi Nasir El-Rufai, wanda ake tuhuma da rashawa kuma aka gurfanar da shi a kotu Kaduna
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Kaduna - Bashir El-Rufai, dan tsohon gwamnan Kaduna Nasir El-Rufai, ya nemi afuwa ga mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima.
Wannan ya biyo bayan wallafa wani sako Da ya yi da ya ke sukar Kashim Shettima a matsayin marar tasiri.

Source: Twitter
Dan El-Rufai ya nemi afuwar Shettima
Hakan na cikin wani sako da ya wallafa a X a yau Lahadi 29 ga watan Maris din shekarar 2026.
A cikin sakon, Bashir ya bayyana cewa kalamansa na baya sun kasance kuskure kuma marasa dacewa, yana mai cewa yana girmama Shettima sosai.
Ya bayyana cewa yana girmama mataimakin shugaban kasar kuma yana mutunta shi fiye da kima.
Ya ce:
"Ina so in yi amfani da wannan dama domin in nemi afuwar Mataimakin Shugaban Najeriya, Mai girma Kashim Shettima, bisa tsohon sakona da na kira shi marar ƙarfi.
"Shi mutum ne da nake matuƙar girmamawa da kuma nake mutuntawa amma na yi kuskure bisa rubutun da na yi.
" Wancan rubutu na rashin tunani ne da na yi ba tare da lura ba."

Source: Twitter
Sakon da Bashir El-Rufai ya rubuta a baya
A cikin asalin sakon da ya wallafa a ranar 6 ga Maris, 2026, wanda daga bisani ya goge, Bashir El-Rufai ya bukaci Shettima ya dauki mataki mai tsauri kan zargin cin hanci da rashawa a Fadar Shugaban Kasa.
Ya rubuta cewa:
“Ina son Shettima. Amma abin takaici, ba shi da jajircewa kwata-kwata.
“Ina fatan wata rana zai gane cewa yana a wani matsayi na musamman, kuma yana da ikon rusa gaba ɗaya tsarin dangin masu cin hanci da laifi a Villa, a gaskiya yana da damar yin hakan.”
Bayan neman afuwar, mutane sun yi martani daban-daban, wasu na yabawa, wasu na sukar sa, amma ya ce babu wata barazana da aka yi masa.
Lamarin ya biyo bayan rikicin siyasa da ya shafi mahaifinsa, wanda ake zargi da rashawa da badakalar kudi, kuma aka gurfanar da shi a kotu Kaduna.
Bashir El-Rufai ya sace guiwar Uba Sani
Mun ba ku labarin cewa a ranar Juma'a, 27 ga watan Maris 2026 aka sanar da rasuwar mahaifiyar tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai.
Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya aika da sakon ta'aziyya ga El-Rufai kan rasuwar Hajiya Umma El-Rufai da ta bar duniya bayan fama da jinya.
Sai dai, jim kadan bayan fitar da sakon ta'aziyyar, wani dan El-Rufai watau Bashir El-Rufai, ya yi masa martani mai zafi.
Asali: Legit.ng

