Kasar Iran Ta Fasa Kwai, Ta Fadi Dalilin Amurka da Isra'ila Na Kai Mata Hari
- Yankin Gabas ta Tsakiya ya tsinci kansa cikin rikici sakamakon yakin da Amurka da Iran suka kaddamar a kan kasar Iran
- Jakadan Iran a Najeriya, Gholamreza Mahdavi Raja, ya bayyana manufar da Amurka da Isra'ila ke son cimmawa sakamakon kai hare-haren
- Gholamreza Mahadavi Raja ya bayyana cewa hare-haren na Amurka da Isra'ila na shafar fararen hula a kasar Iran
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Jakadan Iran a Najeriya, Gholamreza Mahdavi Raja, ya zargi Amurka da yin amfani da rikicin da ake yi da Iran a halin yanzu domin ta samu ikon sarrafa arzikin makamashi na kasar.
Gholamreza Mahdavi Raja ya bayyana ayyukan gwamnatin Amurka a matsayin waɗanda “burin mamaya” ke tunzura su.

Source: Twitter
Jakadan na Iran a Najeriya ya bayyana hakan ne yayin da yake magana a shirin Daily Politics na tashar Trust Tv ranar Litinin, 9 ga watan Maris 2026.

Kara karanta wannan
Tofa: Rigima ta barke tsakanin Amurka da Isra'ila kan yaki da Iran, an ji dalilin sabanin
Me Jakadan Iran ya ce kan Amurka, Isra'ila?
Gholamreza Mahdavi Raja ya ce hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai wa Iran kwanan nan wani ɓangare ne na babban shirin su na mamaye arzikin man fetur na Iran.
“Babban burin Amurka da gwamnatin Isra'ila na wannan zalunci shi ne su ƙwace arzikin makamashin Iran. Gwamnatin Isra'ila tana son ganin rugujewar Iran, su da kansu ne suka sanar da hakan."
- Gholamreza Mahdavi Raja
Duk da hare-haren da aka kai wa ababen more rayuwa, Raja ya ce gwamnatin Iran tana ci gaba da gudanar da ayyukanta yadda ya kamata, kuma al’ummar Iran sun kasance tsintsiya madaurinki ɗaya wajen kare ikon ƙasarsu.
Batun zaben sabon jagoran Iran
Jakadan ya kuma yi watsi da duk wani tasiri na waje wajen zaɓar sabon Jagoran Iran, Ayatollah Mojtaba Khamenei, ɗan marigayi Ayatollah Khamenei, inda ya jaddada cewa:
"Iran ƙasa ce mai cin gashin kanta. Muna yanke shawarwarinmu ne ba tare da tsoma bakin wasu daga waje ba.”
Hare-haren Amurka, Isra'ila na barna a Iran
Game da tasirin yaƙin ga jama'a, jakadan ya zargi makaman Amurka da sauka a wuraren fararen hula, ciki har da wata makaranta a birnin Minab, inda ya yi iƙirarin cewa an kashe yara da dama.
Ya dage kan cewa Iran tana kai hari ne a sansanonin sojoji ne kawai a yankin Gulf, sannan ya zargi Washington da Isra’ila da shirya “makircin ɓoye” domin ɗora wa Tehran laifi.

Source: Twitter
Batun daukar nauyin ta'addanci a Najeriya
Haka kuma Raja ya yi watsi da iƙirarin Isra’ila na cewa Iran tana ɗaukar nauyin ta’addanci a Najeriya, inda ya bayyana hakan a matsayin zargi mara tushe kuma mai nasaba da siyasa.
Jakadan ya jaddada cewa dangantakar Iran da kungiyar harkar Musulunci ta Najeriya ta shafi addini da al'ada ce kawai.
Sanatocin Amurka na son a yi bincike
A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu sanotocin jam'iyyar Democrat na son gwamnatin Amurka ta gudanar da bincike kan wani harin da ake zargin dakarunta sun kai a Iran.
Sanatocin sun yi kiran da a gudanar da bincike kan harin da aka kai wa wata makarantar yara mata a Kudancin Iran wanda ya yi sanadiyyar rasuwar mutum 170.
Manyan sanatocin sun bayyana cewa dole ne ma’aikatar tsaro ta Pentagon ta ba da cikakkun amsoshi game da lamarin wanda ya jawo asarar rayukan fararen hula.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

