Arzikin Abdussamad ya ninku 2, ya doke mutane ya zama attajiri na 3 a Afrika

Arzikin Abdussamad ya ninku 2, ya doke mutane ya zama attajiri na 3 a Afrika

  • Aliko Dangote ya ci gaba da zama mutum mafi arziki a Afrika yayin da dukiyar attajiran nahiyar ta karu sosai a shekarar da ta gabata
  • Wani rahoto da aka fitar ya nuna cewa dukiyar attajiran Afrika 23 ta karu zuwa Dala biliyan $126.7 a shekarar da ta gabata
  • Abdulsamad Rabiu ya samu mafi girman karin dukiya a jerin bayan yawan kadararsa ya tashi da kashi 120%

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT Abuja - Rahoton sabon jerin masu kudin duniya ya nuna cewa attajiran Afrika sun kara karfi a bangaren yawan dukiya.

Rahoton da aka fitar a wannan shekara ta 2026 ya nuna cewa wasu daga cikinsu sun samu karin biliyoyin Daloli a cikin shekara guda.

Kara karanta wannan

Yakin Iran da Amurka ya kara taba Dangote, ya canza farashin fetur karo na 3 a Najeriya

Dukiyar Dangote ta karu, AbdulSamad ya taka sabon matsayi
Shugaban kamfanin BUA AbdulSamad Rabiu, mai sauke simintin Dangote, Alhaji Aliko Dangote Hoto: BUA Group/Dangote Group
Source: Facebook

The Cable a wallafa cewa a cewar rahoton, hamshakin attajirin Najeriya kuma wanda ya kafa kamfanin Dangote, Aliko Dangote, yana cigaba da rike matsayin mutum mafi arziki a Afrika.

Yadda dukiyar Dangote da AbdulSamad ta karu

Channels TV ta wallafa cewa rahoton da mujallar Forbes a fitar ya bayyana cewa dukiyar attajiran Afrika guda 23 ta karu da Dala biliyan 20.3 a cikin shekara daya kacal.

Wannan karin ya kai kusan 21% idan aka kwatanta da shekarar 2025. Dangote ya samu karin dukiya sosai, inda jimillar dukiyarsa ta kai Dala biliyan $28.5.

Wannan ya biyo bayan tashin darajar hannayen jarin kamfanin siminti da kusan 69% tun daga watan Maris na shekarar 2025.

Baya ga haka, kamfanin ya kuma sanar da samun ribar da ta kai Naira tiriliyan daya a shekarar 2025, abin da ya kara karfafa matsayinsa a jerin attajiran nahiyar.

Dangote ya ci gaba da rike kambunsa
Alhaji Aliko Dangote, attajirin Afrika Hoto: Bloomberg
Source: Getty Images

Abdussamad Rabiu ya mallaki N15tr

Kara karanta wannan

Gbajabiamila da yaran Tinubu da suka rike amana yau ake damawa da su a gwamnati

Rahoton ya kuma nuna cewa shugaban rukunin kamfanin BUA, Abdulsamad Rabiu, shi ne ya fi kowa samun karin dukiya a jerin.

Dukiyarsa ta karu da 120% wato kusan Dala biliyan 6.1, inda jimillar dukiyarsa ta kai Dala biliyan 11.2.

A sakamakon ribanyar da arzikinsa ya yi a cikin shekara guda, Alhaji Abdussamad Rabiu ya samu N8.3tr kuma dukiyarsa a yau a lissafin Dala ta kai N15.5tr.

Wannan karin dukiya ya daga AbdulSamad Rabiu daga matsayi na shida zuwa na uku a cikin jerin attajiran Afrika.

A yanzu yana bayan hamshakin attajirin Afirka ta Kudu, Johann Rupert, wanda ya rike matsayi na biyu da dukiyar Dala biliyan $16.1.

Sauran attajiran Najeriya a jerin Forbes

A matsayi na hudu kuwa akwai Nicky Oppenheimer da iyalinsa, wadanda dukiyarsu ta kai Dala biliyan 10.6, bayan da ta karu da kusan Dala miliyan 200 daga Dala biliyan 10.4 a watan Afrilu na 2025.

Dan kasuwar Masar, Nassef Sawiris, wanda ke da hannun jari a kungiyar kwallon kafa ta Aston Villa F.C. kuma yake da kusan kashi 6% a kamfanin Adidas, shi ne na biyar mafi arziki a Afrika da $9.6bn.

Kara karanta wannan

Dalilin gidan gyaran hali na cigaba da tsare Abba Kyari duk da hukuncin kotu

Daga cikin ‘yan Najeriya da suka shiga jerin akwai wanda ya kafa Globacom, Mike Adenuga, wanda ya zo matsayi na shida da $6.5bn, bayan ya sauka daga matsayi na biyar a bara.

Haka kuma shugaban First HoldCo, Femi Otedola, ya sauka zuwa matsayi na 22 da dukiyar da $1.3bn, daga matsayi na 16 da yake a baya.

Dangote ya shirya bunkasa arzikinsa

A baya, mun wallafa cewa fitaccen attajirin dan kasuwa a Afrika, Aliko Dangote, na shirin fadada harkokin kasuwancinsa zuwa wasu fannoni daban-daban.

Dangote na shirin shiga fannin samar da wutar lantarki da karafa don bunkasa samar da masana'antu a nahiyar Afrika da kara fadada kasuwancinsa daga yadda ya ke a yanzu.

Babban dan kasuwar ya kuma bayyana cewa ana shirin kara fadada matatarsa mai tace gangar mai 650,000 a kowace rana Read more:

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng