Kwamishina Ya Yi Murabus daga Mukaminsa a Kano, Ya Mika Takarda ga Gwamna Abba

Kwamishina Ya Yi Murabus daga Mukaminsa a Kano, Ya Mika Takarda ga Gwamna Abba

  • Hon. Umar Haruna Doguwa ya yi murabus daga kujerar kwamishinan Albarkatun Ruwa na jihar Kano a ranar Litinin, 2 ga Fabrairu, 2026
  • Gwamna Abba ya amince da murabus din kwamishinan, tare da yaba masa bisa gudummuwar da ya ba gwamnatinsa da al'ummar Kano
  • Ya yi masa fatan alheri a ayyukansa na gaba, sannan ya tabbatar da cewa gwamnatin Kano za ta ci gaba da dora wa kan nasarorin ya samu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da murabus din Kwamishinan Albarkatun Ruwa na jihar, Umar Haruna Doguwa.

Hon. Umar Haruna Doguwa ya mika takardar murabus dinsa ne a hukumance ranar Litinin, 2 ga watan Maris, 2026, wanda matakin ya fara aiki daga yau.

Gwamna Abba.
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf yayin ganawa da kwamishinoni a gidan gwamnati Hoto: Sanusi Bature
Source: Facebook

Abba ya amince da murabus din Doguwa

Kara karanta wannan

Yaron Atiku ya yi murabus daga gwamnatin Adamawa bayan sauya shekar gwamna

Wannan yana kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya sanya wa hannu a ranar Talata kuma ya wallafa a Facebook.

Gwamna Abba ya nuna matukar godiyarsa ga Hon. Doguwa saboda jajircewarsa, biyayya, da kuma kwazon da ya nuna wajen yi wa al'umma da gwamnatin jihar Kano hidima.

Gwamnan ya tuna cewa Hon. Doguwa ya taba rike mukamin Kwamishinan Ilimi, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen ciyar da manufofi da sauye-sauyen ilimi gaba, ciki har da ayyana dokar ta-baci, kafin a mayar da shi Ma'aikatar Albarkatun Ruwa.

Nasarorin da tsohon kwamishinan ya samu

Ya lura cewa a cikin shekara guda da ya shafe yana jagorantar Ma'aikatar Ruwa, an samu manyan nasarori wajen gyara ababen samar da ruwa da kuma fadada samar da ruwan sha ga mutane a fadin jihar.

Abba ya kara da cewa jagorancin Hon. Doguwa ya taimaka wajen karfafa hukumomin da ke karkashin ma'aikatar tare da inganta ayyuka daidai da burin gwamnati na samar da ruwa mai tsafta.

Gwamnan ya bayyana Hon. Doguwa a matsayin ma'aikacin gwamnati mai tarbiyya da kwazo, wanda gudunmawarsa za ta kasance daya daga cikin nasarorin da wannan gwamnati ta samu.

Kara karanta wannan

APC ko ADC: Gwamna ya gaji da rikicin PDP, ya fara shirin sauya sheka don zaben 2027

Gwamna Abba.
Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano a wani taro a gidan gwamnati Hoto: Sanusi Bature D-Tofa
Source: Facebook

Gwamna ya yi wa Hon. Doguwa fatan alheri

Ya yi masa fatan alheri a ayyukansa na gaba, sannan ya tabbatar da cewa gwamnatin Kano za ta ci gaba da dora wa kan nasarorin da aka samu a bangaren albarkatun ruwa.

Gwamna Abba ya sake jaddada kudurin gwamnatinsa na tabbatar da samar da ruwan sha mai tsafta da kuma inganta jin dadin al'ummar jihar Kano.

Sakamakon haka, Gwamnan ya umarci kwamishinan Ilimi, Gwani Dr. Ali Haruna Abubakar Makoda, da ya kula da Ma'aikatar Ruwa har zuwa lokacin da za a nada sabon kwamishina.

An ba da hutun karamar Sallah a Kano

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin Kano ta bada hutun Sallah ga makarantun gwamnati da na masu zaman kansu da ke a fadin jihar.

Ma’aikatar Ilimi ta jihar Kano ta ayyana ranar Lahadi, 1 ga watan Maris, 2026, a matsayin ranar da za a fara hutun ƙaramar Sallah.

Gwamnati ta ba da umarnin cewa iyaye da masu lura da ɗaliban da ke makarantun kwana su kwashe yaransu tun daga safiyar ranar Juma'a, 27 ga watan Fabrairu, 2026.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262