Sarakuna Sun Shiga Uku, Gwamna Ya Yi Masu Barazanar Raba Wasu da Kujerunsu

Sarakuna Sun Shiga Uku, Gwamna Ya Yi Masu Barazanar Raba Wasu da Kujerunsu

  • Gwamnan Akwai Ibom, Umo Eno ya yi barazanar kwace takardun sarautar sarakunan gargajiya a fadin jihar game da kayan gwamnati
  • Eno ya ce duk shugaban ƙauye da ya kasa kare makarantu ko kayayyakin gwamnati ba shi da amfani a matsayinsa
  • Ya umarci jami’ai su kira taron gaggawa da shugabannin ƙauyuka domin sanar da su sabon matakin da aka dauka

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Uyo, Akwa Ibom - Gwamnan jihar Akwa Ibom, Umo Eno, ya yi barazana ga wasu sarakunan gargajiya a jihar game da barnata kayan gwamnati.

Gwamnan ya ce zai janye takardun shaidar sarauta na duk wani shugaban ƙauye idan aka samu lalata dukiyar gwamnati a yankinsa.

Gwamna ya yi wa sarakunan gargajiyan barazana a Akwa Ibom
Gwamna Umo Eno na jihar Akwa Ibom. Hoto: Pastor Umo Eno.
Source: Facebook

Gwamna ya yi barazana ga sarakunan gargajiya

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin taron addu’ar wata-wata da aka gudanar a Fadar Gwamnati da ke Uyo, inda ya jaddada cewa ba za a lamunci barna ba, cewar Punch.

Kara karanta wannan

Rikicin APC: Majalisa ta fara yunkurin tsige mataimakin gwamna? Aiyedatiwa ya yi bayani

Ya ce duk ƙauyen da gwamnati ta kai ayyuka, amma aka bari ɓata-gari suna lalata kayayyaki, to za a hukunta shugaban ƙauyen ta hanyar kwace takardarsa.

A cewarsa, idan makarantar gwamnati mai kayan aiki na zamani ta lalace cikin sauƙi a ƙauyen mutum, hakan na nuna rashin kulawa daga shugabannin yankin.

Gwamnan ya umarci Kwamishinan Ƙananan Hukumomi da Harkokin Sarauta, Frank Archibong, da shugaban ALGON na jihar, Dr. Uwemedimo Udo, su kira taro da shugabannin ƙauyuka domin yi musu bayani.

Ya kuma bukaci al’ummar jihar da su kasance masu lura da tsaro tare da kare dukiyar jama’a daga lalacewa.

Game da shirin samar da kananan ayyukan ruwa a kowace mazaba, Gwamna Eno ya ce kwamitin Inter-Ministerial Direct Labour Committee ne zai kula da aiwatar da su.

A yayin huduba mai taken “Unsearchable God,” daga littafin Romawa 11:33, Bishop Bolaji Adeisrael ya jaddada cewa hanyoyin Allah abin mamaki ne amma suna alheri ga bayinsa.

Taron addu’ar ya samu halartar mataimakin gwamna, Sanata Akon Eyakenyi, da sauran manyan jami’an gwamnati da shugabannin addini a jihar.

Game da shirin samar da kananan ayyukan ruwa a kowace mazaba, Gwamna Eno ya ce kwamitin Inter-Ministerial Direct Labour Committee ne zai kula da aiwatar da su.

Kara karanta wannan

Kwanaki 3 da shiga watan Ramadan, mutane sun fara fuskantar matsala a jihar Kano

A yayin huduba mai taken “Unsearchable God,” daga littafin Romawa 11:33, Bishop Bolaji Adeisrael ya jaddada cewa hanyoyin Allah abin mamaki ne amma suna alheri ga bayinsa.

Taron addu’ar ya samu halartar mataimakin gwamna, Sanata Akon Eyakenyi, da sauran manyan jami’an gwamnati da shugabannin addini a jihar.

Sarki ya mutu ana tsaka da rigimar sarauta

Mun ba ku labarin cewa an shiga jimami bayan sanar da mutuwar babban Sarki da ya shafe shekaru yana gwagwarmaya kan rikici game da kujerarsa da har yau ba ta kare ba.

Al’ummomin Egrangbene a Burutu, jihar Delta, sun sanar da rasuwar zababben Sarki, Henry Ambakederemo Okrikpa, yana da shekaru 70.

An ayyana zaman makoki gaba ɗaya a yankin, yayin da rikicin sarauta ya daɗe tun bayan naɗinsa a 2009, amma gwamnatin Delta ba ta amince da shi ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.