Halin da Ake Ciki yayin da El Rufai Ke Ci Gaba da Zama Tsare a Hannun ICPC
- Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a tsare a hannun hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC
- Hukumar ICPC ta cafke tsohon gwamnan na Kaduna ne tare da tsare shi domin gudanar da bincike kan wasu zarge-zarge da ake yi masa
- Ci gaba da tsare El-Rufai na zuwa ne bayan ya samu beli daga wajen hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC bayan ya kwashe kwana biyu a hannunta
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, na ci gaba da sake zama a tsare a hannun hukumar ICPC.
Ana sa ran zai kwashe dare na biyu a hannun hukumar ICPC, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike.

Source: Twitter
Jaridar Vanguard ta kawo rahoton cewa har zuwa yammacin ranar Alhamis, 19 ga watan Fabrairun 2026 babu wani rahoton tabbatar da an sake shi.
El-Rufai na hannun hukumar ICPC
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawar ta tabbatar da tsare shi tun da fari a cikin wata sanarwa da shugaban sashen yaɗa labarai da sadarwa na hukumar, Mista Okor Odey, ya sanya wa hannu.
ICPC ta fitar da sanarwar ne a shafinta na X kan tsare tsohon gwamnan na jihar Kaduna.
“Hukumar ICPC tana sanar da cewa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, yana hannunmu har zuwa lokacin tashi daga aiki a yau Laraba, 18 ga watan Fabrairu, 2026. Malam Nasir El-Rufai yana tsare ne a hukumar dangane da wasu bincike da ake gudanarwa."
- Okor Odey
Ana ci gaba da bincikar El-Rufai
To sai dai kuma, majiyoyi masu masaniya kan lamarin sun bayyana cewa har yanzu masu bincike suna tattaunawa da tsohon gwamnan.
Wata majiya ta ce:
“Suna gudanar da tsarin bincike na yau da kullum, wanda ya haɗa da yi masa tambayoyi, karɓar bayanansa a karkashin doka, da kuma duba takardun kuɗi da na ayyukan da aka gudanar a lokacin gwamnatinsa.”
Ci gaba da tsare El-Rufai a hannun ICPC ya biyo bayan abubuwan da suka faru a farkon wannan makon, bayan ya amsa gayyatar hukumar EFCC kan zargin karkatar da kuɗaɗe da ya shafi lokacin mulkinsa tsakanin 2015 zuwa 2023.

Source: Twitter
EFCC ta fara tsare El-Rufai
Ya kwashe dare biyu a babban ofishin EFCC da ke Abuja ana yi masa tambayoyi kan wasu ma’amaloli da ayyukan da aka gudanar a lokacin mulkinsa.
Hukumar EFCC ta ba wa El-Rufai belin gaggawa a yammacin ranar Laraba bayan kammala zagayen farko na tambayoyin.
To sai dai jim kaɗan bayan nan, wasu jami’ai masu ɗauke da makamai da aka jibge a wajen ofishin hukumar suka sake kama shi dangane da wani binciken na daban.
Hakeem Baba-Ahmed ya fadi matsalar El-Rufai
A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon mai ba mataimakin shugaban kasa shawara kan harkokin siyasa, Hakeem Baba-Ahmed, ya yi magana kan Nasir El-Rufai.
Hakeem Baba-Ahmed ya soki tsohon gwamnan na Kaduna, kan matakan da yake ɗauka yayin da yake fuskantar zarge-zargen cin hanci da rashawa.
Tsohon hadimin mataimakin shugaban kasar ya bayyana cewa Nasir El-Rufai mutum ne mara daukar shawara.
Asali: Legit.ng

