An ga Watan Azumin Ramadan a Najeriya, Sarkin Musulmi Ya Fitar da Sanarwa
- Sarkin Musulmi, Sa'ad Abubakar III, ya tabbatar da ganin jinjirin Ramadan, ya ayyana 18 ga Fabrairu a matsayin ranar farko ta azumi
- Shehun Borno, Abubakar Ibn Umar Garbai El-Kanemi, ne ya sanar da ganin watan a madadin Sarkin Musulmi
- An ce Sarkin Musulmi ya wakilta Shehun Borno ne saboda tafiyarsa ƙasa mai tsarki domin gudanar da ibadar Umrah
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Maiduguri, Borno - Kwamitin ganin wata a Najeriya ya fitar da sanarwa kan ganin watan Ramadan domin fara azumi a kasar.
Sarkin Musulmi, Muhammad Sa'ad Abubakar III ya tabbatar da ganin jinjirin watan Ramadan a Najeriya a daren yau Talata 17 ga watan Faburairun 2026.

Source: Facebook
Hakan na cikin wata sanarwa da shain kwamitin ganin wata a Najeriya ya wallafa a X a yau Talata 17 ga watan Faburairun 2026.
Sarkin Musulmi ya tabbatar da ganin watan Ramadan
An tabbatar da ganin watan a yau Talata 17 ga watan Faburairun 2026 bayan wasu amintattu sun tabbatar da ganin wata a yankunansu.
Sanarwar da aka fitar da kawo karshen watan Sha'aban tare da tabbatar da shiga Ramadan wacce ta kasance mafi girma da daraja a cikin sauran watannin Musulunci.
"SANARWAR GANIN JINJIRIN RAMADAN!
"Assalamu alaikum,
"Mai Martaba ya tabbatar da ganin jinjirin watan Ramadan a Najeriya, kuma ya ayyana cewa gobe, 18 ga Fabrairu, za ta zama ranar farko ta Ramadan 1447AH."

Source: Facebook
Shehun Borno ya sanar da ganin watan Ramadan
Wani mai amfani da shafin X, Imran Muhammad ya wallafa bidiyon sanar da ganin watan Ramadan da aka yi a daren yau Talata 17 ga watan Faburairun 2026.
Mai Martaba, Shehun Borno, Alhaji (Dr.) Abubakar Ibn Umar Garbai Al-Amin El-Kanemi shi ya tabbatar da ganin watan domin fara azumin Ramadan.
Basaraken ya sanar da ganin wata a madadin Sarkin Musulmi, Mai Alfarma, Muhammad Sa'ad Abubakar III bayan wakilta shi.
Majiyoyi sun tabbatar da cewa Sarkin Musulmi ya wakilta Shehun Borno bayan ya tafi kasar mai tsarki domin gudanar da ibadar Umrah.
Saudiyya ta tabbatar da ganin watan Ramadan
Mun ba ku labarin cewa Gwamnatin kasar Saudiyya ta sanar da cewa an ga watan Ramadan a yammacin yau Talata, 17 ga watan Fabrairun shekarar 2026.
Hakan na zuwa ne bayan fara duba jinjirin wata da hukumomin kasar suka yi bisa umarnin da gwamnati ta bayar ga 'yan kasar baki daya.
An samu rahotanni game da sakamakon duba watan Ramadan a wasu kasashen Musulmi da sauransu da ke fadin duniya a yau Talata 17 ga watan Faburairun 2026.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

