Tinubu Ya ba da Umarni kan Gobarar da Ta Babbake Kasuwar Kano
- Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jajantawa al'ummar Kano kan iftila'in gobara da ya afku a jiya Asabar 14 ga watan Fabrairun 2026
- Tinubu ya ba da umarnin gudanar da cikakken bincike kan gobarar da ta sake aukuwa a Kasuwar Singer ta Kano
- Ya nuna alhini kan yadda gobarar ta sake faruwa karo na biyu cikin makonni biyu, yana mai cewa lamarin ya zama abin damuwa
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Abuja - Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi alhini game da abin bakin ciki da ya faru a Kano a jiya Asabar 14 ga watan Fabrairun 2026.
Tinubu ya umarci a gudanar da cikakken bincike kan yawaitar gobarar da ke tashi a Kasuwar Singer da ke Kano.

Source: Facebook
Tinubu ya tura sako game da gobara a Kano
Hakan na cikin wata sanarwa da hadiminsa a bangaren yada labarai, Bayo Onanuga ya wallafa a X a yau Lahadi 15 ga watan Fabrairun 2026.
Hakan ya biyo bayan sabuwar gobara ta lalata dukiyoyin al'umma da ta ci har safiyar yau Lahadi 15 ga watan Fabrairun 2026.
Shugaban ya bayar da wannan umarni ne bayan gobarar da ta tashi a yammacin ranar Asabar ta ci gaba har zuwa safiyar Lahadi, inda ta jawo asara mai yawa ga ’yan kasuwa, Tinubu ya ce maimaituwar gobarar na jefa ’yan kasuwa cikin bakin ciki.
Sanarwar ta ce shugaban ya tuntubi gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, domin samun cikakken rahoto kan lamarin da ya bayyana a matsayin abin takaici.

Source: Facebook
Halin da Tinubu ya shiga kan gobarar
An ce Shugaban ya damu matuka da cewa sabuwar gobarar ta faru ne kasa da makonni biyu bayan wata gobara ta lalata shaguna da kadarori da dama a kasuwar.
Sanarwar ta ce:
"Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya jajanta wa ’yan kasuwa da al’ummar Jihar Kano kan mummunar gobarar da ta tashi a kasuwar Singer ta Kano a ƙarshen mako.
" Shugaban ƙasar ya nuna matuƙar damuwa ganin cewa wannan lamari ya faru ne kasa da makonni biyu bayan wata gobara ta lalata shaguna da dukiyoyi masu yawa a kasuwar.
"Tinubu ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan musabbabin gobarar kasuwannin, waɗanda sau da dama ke jefa ’yan kasuwa cikin halin ƙunci da takaici."
Ya jajanta wa ’yan kasuwar da al’ummar jihar Kano, yana mai tabbatar musu da kulawar gwamnatin tarayya yayin da hukumomi ke tantance asara da daukar matakan kariya.
Kwankwaso ya jajanta wa yan kasuwar Singer
Kun ji cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya nuna alhini kan sabuwar gobarar da ta tashi a kasuwar Singer da ke Kano a ranar Asabar 14 ga watan Fabrairun 2026.
Tsohon gwamnan Kano ya aike da sakon jaje ga ‘yan kasuwar da suka yi asara, yana kira da a kawo daukin gaggawa.
Kwankwaso ya roki hukumomi, jami’an tsaro da masu hannu da shuni su hada kai wajen tallafa wa wadanda abin ya shafa domin saukaka masu.
Asali: Legit.ng

