Mutane na cikin Hada Hada, Gobara Ta Sake Kamawa Rigi Rigi a Fitacciyar Kasuwa a Kano

Mutane na cikin Hada Hada, Gobara Ta Sake Kamawa Rigi Rigi a Fitacciyar Kasuwa a Kano

  • A karo na biyu cikin kasa da makonni biyu, kasuwar Singa da ke cikin jihar Kano ta sake fuskantar ibtila'in gobara yau Asabar
  • Rahotanni daga yan kasuwa sun nuna cewa gobarar ta kama ne a sashen Gidan Glass da misalin karfe 4:00 na yamma
  • Babu wata sanarwa a hukumance kawo yanzu amma majiyoyi sun tabbatar da cewa motar 'yan kwana-kwada daya kacal ta ka dauki kasuwar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Rahotanni sun nuna cewa 'yan kasuwa sun sake gamuwa da ibtila'in gobara a fitacciyar kasuwar nan ta Singa da ke cikin birnin Kano.

An ruwaito cewa gobarar ta lalata shaguna da dama a sashen Gidan Glass na kasuwar da ke kan titin Ado Bayero, kusa da Murtala Muhammad Way.

Jihar Kano.
Taswirar jihar Kano da ke Arewa maso Yammacin Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa lamarin, wanda ya fara da yammacin ranar Asabar, 14 ga watan Fabrairu, 2026, shi ne karo na biyu da gobara ke tashi a kasuwar cikin ƙasa da makonni biyu.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga 200 sun shiga garuruwa 3 da Asubah, sun kashe mutane sama da 30

Gobara ta kama a kasuwar Singa

Wani ɗan kasuwa, Nasir Maharazu, ya shaida wa manema labarai cewa gobarar ta fara ne da misalin ƙarfe 4:00 na yamma, kuma har zuwa lokacin da ake haɗa wannan rahoto, wutar na ci gaba da ci a Singa.

Ya ce:

“Yanzu da nake magana da ku, ina ganin wutar tana ci. Dukkan ginin bene mai hawa biyu ya kama da wuta. Wannan gobara ma ta fi wadda ta tashi a kasuwar cikin makonni biyu da suka gabata muni.”

A lokacin haɗa wannan rahoto, an ga motar kashe gobara guda ɗaya kacal a wurin da lamarin ya faru.

Kasuwar Singa ita ce mafi girman kasuwar kayan abinci a Kano da ma Arewacin Najeriya, tana samar da kayan masarufi da abinci ga yawancin jihohin Arewa da ma wasu ƙasashen Yammaci da Tsakiyar Afirka.

Karin bayani na nan tafe...

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262