Tofa: Gwamna Ya Rufe Dukkan Makarantu, Ya Sanya Dokar Zaman Gida Ta Awanni 20
- Gwamnan Ebonyi, Francis Nwifuru, ya rufe dukkan makarantu a yankin Amasiri tare da sanya dokar hana fita na awanni 20 bayan mummunan hari
- Rahoto ya ce harin ya yi sanadin kisan mutane hudu da yanke musu kai, tare da kona gidaje sama da tara a kauyen Okporojo
- Gwamnatin Ebonyi ta tube sarakunan gargajiya biyu tare da rushe dukkan shugabancin al’umma a Amasiri domin dawo da doka da oda
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Abakaliki, Ebonyi - Gwamnan Jihar Ebonyi, Francis Nwifuru, ya bayar da umarnin rufe dukkan makarantu a wasu yankuna a jihar.
Gwamnan ya dauki wannan mataki ne a yankin Amasiri da ke Karamar Hukumar Afikpo, tare da sanya dokar hana fita ta awanni 20 a kullum.

Source: Facebook
Dalilin daukar matakan a Ebonyi
Da yake zantawa da ’yan jarida bayan taron majalisar tsaro a Abakaliki, gwamnan ya bayyana jerin matakan tsaro da na gudanarwa domin dawo da zaman lafiya da hana sake faruwar irin wannan hari, cewar Punch.
Matakin ya biyo bayan wani mummunan hari da aka kai a kauyen Okporojo, da ke cikin yankin Oso Edda a Karamar Hukumar Edda, wanda ake zargin wasu ’yan ta’adda daga Amasiri ne suka kai harin.
Rahotanni sun nuna cewa harin ya yi sanadin kisan mutane hudu tare da yanke musu kai, yayin da aka kona gidaje fiye da tara a yankin.
An yanke wadannan matakai ne bayan taron gaggawa da Majalisar Tsaron Jihar Ebonyi ta gudanar a daren ranar Asabar, domin daukar matakan da za su kawo karshen tashin hankalin.
Tun da farko a ranar Asabar, Gwamna Nwifuru ya ziyarci yankin da abin ya shafa, inda ya jajanta wa mazauna yankin, tare da umartar jami’an tsaro da su kama tare da gurfanar da duk wadanda ke da hannu a harin.
Nwifuru ya kara da cewa majalisar ta bayar da umarnin rushe dukkan tsarin shugabancin al’umma a yankin, ciki har da shugabannin kungiyoyin ci gaba, hakimai, shugabannin mata da na matasa, tare da duk wata kungiya ta hukuma ko ba ta hukuma ba.

Source: Original
Umarnin da Gwamna ya bayar a Ebonyi
Gwamnan ya ce an umarci shugabannin kananan hukumomin Afikpo, Ivo, Ohaozara da Onicha da su karbi ragamar tafiyar da harkokin mulki a Amasiri har zuwa wani lokaci.
“Gwamnati ta amince da shawarar majalisar, ta rushe dukkan shugabannin kungiyoyin ci gaba, hakiman kauyuka, shugabannin mata da na matasa, kungiyoyin matasa, mata da sauran kungiyoyi a Amasiri.”
Ya kara da cewa an bayar da umarnin rufe dukkan cibiyoyin gwamnati a yankin, ciki har da makarantu masu zaman kansu da na gwamnati, da kuma Cibiyar Ci gaban Amasiri.
Nwifuru ya ce an shirya kudurin doka da za a mika wa Majalisar Dokokin Jihar Ebonyi domin soke dokar da ta kafa Cibiyar Ci gaban Amasiri.
A cewarsa:
“Daga gobe da safe, ba za a sake yin karatu a Amasiri ba, kuma ba za a sake samun cibiyar ci gaba a yankin ba.”
Gwamnan ya kara da cewa an sanya dokar hana fita a Amasiri daga karfe 2:00 na rana zuwa karfe 10:00 na safe a kowace rana.
A karkashin dokar, dukkan kasuwanni, shaguna, bankuna, wuraren kasuwanci, ma’adinan dutse da sauran harkokin kasuwanci za su kasance a rufe a lokutan da aka kayyade.
Gwamna ya tube Sarki, ya kori mukarrabansa
Mun ba ku labarin cewa Gwamna Francis Nwifuru ya fusata matuka kan mummunan farmakin da aka kai kauyen Okporojo, wanda ya yi sanadiyyar kashe mutane hudu.
Rahotanni sun nuna cewa mutanen garin Amasiri ne suka kai harin, saboda rikicin da ke tsakaninsu da kauyen Okporojo.
Gwamna Nwifuru ya tsige sarkin yankin tare da korar duk wani dan garin Amasiri da ke rike da mukami a gwamnatinsa.
Asali: Legit.ng


