Kotu Ta Hukunta Makiyayan da Suka Saki Dabbobi a Gonakin Manoma
- Wata kotu ta musamman a jihar Jigawa ta yanke hukunci kan wasu makiyaya da ake zargi da sakin dabbobinsu a gonakin manoma
- Kotun ta samu makiyayan da laifuffuka a shari'ar wadda kwamishinan 'yan sanda na jihar Jigawa ya shigar a gabanta
- Alkalin kotun ya umurci su biya diyya ta miliyoyin Naira tare da ba su wa'adin kwanakin da za su daukaka kara
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Jigawa - Wata kotu ta musamman kan rikicin manoma da makiyaya a jihar Jigawa ta yanke hukunci kan shari'ar da aka shigar a gabanta.
Kotun ta umurci makiyaya tara da su biya diyya ta Naira miliyan 500 ga manoman da amfanin gonakinsu ya lalace a karamar hukumar Birnin Kudu.

Source: Original
Jaridar TheCable ta ce alkalin kotun, Yusuf Abubakar, ne ya yanke hukuncin a ranar Talata, 20 ga watan Janairun 2026.

Kara karanta wannan
An bada umarnin kama tsohon hadimin gwamna da mutum 4 kan zargin alaka Bello Turji
Kotu ta samu makiyaya da laifi
Yusuf Abubakar ya jingina hukuncin da tanade-tanaden dokar 'Penal Code', ciki har da sashe na 78, 19 da 322.
Shari’ar wadda kwamishinan ‘yan sanda na jihar Jigawa ya shigar, ta shafi Ilu Adamu da wasu makiyaya takwas, kuma ta shafe fiye da shekaru biyu ana shari’a kafin yanke hukunci.
Rahoton Premium Times ya bayyana cewa an tuhumi wadanda ake zargin da laifuffuka hudu, ciki har da barin shanunsu su shiga gonakin noma ba bisa ka’ida ba.
Lamarin da ya jawo babbar asarar amfanin gona, wanda hakan ya saba wa sashe na 97 na 'Penal Code'.
Laifuffukan da aka samu makiyayan da su
A hukuncinsa, alkalin ya kuma dora laifi a kan wadanda ake tuhumar bisa lalata kadarorin shugaban kungiyar manoman Najeriya (AFAN) na jihar Jigawa.
Kotu ta tabbatar da cewa makiyayan sun kona tayar tarakta da babur mallakar shugaban AFAN, inda ta umurce su da su biya Naira dubu 500 a matsayin diyya.
Alkalin ya kara da cewa wadanda ake tuhumar sun ji wa wasu manoma rauni, abin da ya saba wa sashe na 332 da 114 na dokar Penal Code.
Bayan nazarin hujjojin da masu gabatar da kara suka gabatar, kotun ta samu makiyayan da laifi a dukkan tuhume-tuhumen da ake yi musu.

Source: Getty Images
Wane hukunci kotu ta yanke?
Sakamakon haka, kotun ta umurci wadanda aka samu da laifi da su biya Naira miliyan 500 a matsayin diyya ga manoman da abin ya shafa, tare da ba su wa’adin kwanaki 30 domin daukaka kara kan hukuncin.
Lamarin da ya kai ga wannan shari’a ya faru ne a dazuzzukan Kwarsa, Larau da Tukuda da ke karamar hukumar Birnin Kudu.
Wadannan yankuna sun dade suna fuskantar rikice-rikice tsakanin manoma da makiyaya kan batun amfani da filaye da wuraren kiwo.
'Yan bindiga sun tarwatsa makiyaya
A wani labarin kuma, kun ji cewa 'yan bindiga dauke da makamai sun kai hare-hare kan Fulani makiyaya a jihar Plateau.
Mummunan harin na 'yan bindiga ya haifar da sace shanu kimanin 168 tare da tarwatsa makiyayan da ke kiwo a yankunan da ke karamar hukumar Barikin Ladi.
Tsagerun yan bindigan sun afka wurin kiwo suna harbe-harbe, abin da ya tilasta makiyaya tserewa domin kare rayukansu, yayin da maharan suka tsere da dabbobin.
Asali: Legit.ng
