Rai Bakon Duniya: An Yi Jana'izar Sanata bayan Ya Rasu a Asibitin Kasar India

Rai Bakon Duniya: An Yi Jana'izar Sanata bayan Ya Rasu a Asibitin Kasar India

  • An yi jana'iza tare da birne marigayi sanatan Nasarawa ta Arewa, Godiya Akwashiki a gidansa da ke birnin Lafiya yau Asabar
  • Sanata Godiya Akwashiki ya rasu ne bayan fama da jinya a wani asibiti a kasar Indiya, yana da shekaru 52 da haihuwa
  • Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, wanda ya halarci jana'izar, ya ce rasuwar Sanatan babban rashi ne ga Najeriya baki daya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Nasarawa, Nigeria - An yi jana'izar Sanata Godiya Akwashiki (SDP, Nasarawa ta Arewa) a gidansa da ke birnin Lafia, inda iyalai, abokan aiki da manyan ’yan siyasa suka yi masa bankwana.

Sanata Akwashiki ya rasu ne a ranar 31 ga Disamba, 2025, yana da shekaru 52, bayan fama da doguwar jinya a wani asibiti a ƙasar Indiya.

Sanata Akwashiki.
Sanatan Nasarawa ta Arewa, Marigayi Godiya Akwashiki Hoto: Godiya Akwashiki
Source: Twitter

An birne Sanatan Nasarawa a gidansa

Kara karanta wannan

ADC ta samo hanyar ceto Najeriya daga hannun Shugaba Tinubu

Daily Trust ta rahoto cewa an yi jana’izarsa da misalin karfe 1:50 na rana yau Asabar, bayan gudanar da taron addu'o'i a Cocin St. William Cathedral da ke Lafia, kafin a birne shi a harabar gidansu.

Marigayin, wanda aka haife shi a Angba Iggah da ke ƙaramar hukumar Nasarawa Eggon ta Jihar Nasarawa, ya fara zama Sanata a shekarar 2019, sannan aka sake zaɓarsa a 2023.

Kafin haka, ya taba zama ɗan Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa, inda ya riƙe muƙamin shugaban masu rinjaye, sannan daga bisani ya zama Mataimakin Kakakin Majalisar.

Gwamna Sule ya yi alhinin Akwashiki

Da yake jawabi a wajen jana’izar, Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya bayyana marigayin a matsayin jagora mai sadaukarwa, wanda ya ba da rayuwarsa wajen bautar Allah da yi wa al’umma hidima.

“Mun hallara a nan ne domin yi wa Sanata Godiya Akwashiki bankwana na ƙarshe, mutuwa tana tunatar da mu, mu kasance masu tawali’u da ƙaunar juna,” in ji Gwamna Sule.

Ya yi addu’ar Allah ya ba iyalansa, al’ummar Eggon da kuma ƙasar baki ɗaya haƙurin jure wannan babban rashi, tare da kira ga ’yan Najeriya da su rungumi yafiya domin ci gaban ƙasa.

Kara karanta wannan

Wace cuta ke damunsa? An kwantar da Sarkin Saudiyya a asibiti, sanarwa ta fito

Wurin jana'iza.
Gwamna Abdullahi Sule, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio da wasu jiga-jigai a jana'izar Sanata Akwashiki Hoto: @BarauIJibrin
Source: Twitter

Sanata Barau ya wakilci Akpabio

A nasa jawabin, Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, wanda Mataimakin Shugaban Majalisar, Sanata Barau Jibrin, ya wakilta, ya ce Najeriya ta yi babban rashi.

“Mun rasa ɗan’uwa, aboki kuma abokin aiki wanda ya bayar da gagarumar gudummawa ga ci gaban jama'a a mazabarsa da ƙasa baki ɗaya,” in ji Barau.

Sanata Barau ya yi addu’ar Allah ya ba iyalansa, Nasarawa ta Arewa da Najeriya juriyar wannan rashi da ba za a iya maye gurbinsa ba, kamar yadda Vanguard ta rahoto.

Za a yi janazar mataimakin gwamnan Bayelsa

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin jihar Bayelsa ta kammala shirye-shiryen jana'izar mataimakin gwamna, Mr Lawrence Ewhrudjakpo.

A ranar Alhamis, 11 ga watan Disamba, 2025, Ewhrudjakpo ya yanke jiki ya fadi a ofishinsa da ke cikin gidan gwamnatin Bayelsa , inda aka garzaya da shi asibitin tarayya (FMC) amma rai ya yi halinsa.

Gwamna Douye Diri, ya sanar da cewa za a gudanar da jana'izar tsohon mataimakinsa, Marigayi Lawrence Ewhrudjakpo, a ranar 30 ga watan Janairu, 2026.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262