Wata Sabuwa: An Bude Sabon Bincike bayan Gano Bindigogi da Alburusai a Gidan Malami
- An sake bude sabon bincike kan tsohon M inistan shari'a, abubakar Malami bayan samamen da hukumar EFCC ta kai gidansa a jihar Kebbi
- Wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa jami'an EFCC sun gano bindigu da alburusi a gidan malami da ke cikin birnin Kebbi
- Rahoto ya nuna cewa har yanzu Malami bai cika sharuddan belin da babbar kotun tarayya ta ba shi ba, yana tsare a gidan yarin Kuje da ke Abuja
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS) ta fara binciken Tsohon Antoni Janar kuma Tsohon Ministan Shari'a, Abubakar Malami (SAN) kan wasu makamai da aka gano a gidansa.
An ruwaito cewa Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta ci karo da bindigu da alburusai lokacin da ta kai samame gidan Malami da ke birnin Kebbi.

Source: Facebook
An gano makamai a gidan Abubakar Malami
Jaridar The Nation ta ruwaito cewa hukumar ta mika makaman ga Hukumar DSS don gudanar da cikakken bincike, domin ba ƙarƙashin hurumin EFCC ba ne.
Ba a bayyana adadin makamai da harsasan da aka gano ba a halin yanzu, amma rahotanni sun nuna cewa adadinsu ya kai kololuwa da zai jawo cikakken bincike daga DSS.
Malami, wanda aka ba da belinsa a makon da ya gabata tare da dansa Abdulaziz, da matarsa, har yanzu yana tsare a Gidan Gyaran Hali na Kuje, saboda bai cika sharuddan belin ba.
Malami na neman kaucewa jami'an DSS
Amma wasu majiyoyi sun ce yana ɗaukan matakai a hankali domin jinkirta binciken DSS kan makaman da aka samu a gidansa.
“An fara binciken tsohon ministan kan yadda aka ga makamai a gidansa na Birnin Kebbi. Tuni dai aka mika jerin abubuwan da aka gano ga hukumar DSS.
"Yanzu ya rage ga Malami ya bayyana wa DSS yadda ya samu makaman, wanda shi ya sa bai cika sharuddan belinsa ba. Yana cikin gidan yari ne domin kaucewa yiwuwar kama shi da DSS ka iya yi.
"Jami’an DSS sun je har cikin kurkukun Kuje domin gayyatar Malami, amma ya samu labarin zuwansu, ya tayar da hankali. Amma dai dole doka zata yi aiki.”
Wata majiya daga cikin hukumar EFCC ta tabbatar da cewa har yanzu Malami bai cika sharuddan belinsa ba, in ji rahoton Punch.

Source: Facebook
Yaushe aka fara binciken Malami?
Majiyar ta kara da cewa an fara binciken ayyukan Malami ne tun a lokacin da tsohon shugaban EFCC Ibrahim Magu, yake ofis.
“An ci gaba da binciken har lokacin shugaban rikon kwarya, Ibrahim Chukkol, zuwa shugaban EFCC na yanzu Olukoyede.
"Babu wani abu na hassada a binciken da EFCC ke yi wa Malami tun 2019. Malami ya san wannan lamari," in ji majiyar.
Kotu ta ba da belin Abubakar Malami
A wani rahoton, kun ji cewa Babbar Kotun Tarayya ta ba da belin tsohon babban lauyan gwamnatin tarayya, kuma Ministan shari'a, Abubakar Malami.
Mai shari'a Bello Kawu ne ya amince da buƙatar belin a ranar Talata, biyo bayan wani koke da lauyoyin Malami suka shigar gabansa.
A cewar kotun, an bayar da belin Malami ne a kan sharuɗɗa irin waɗanda EFCC ta gindaya a baya, waɗanda suka haɗa da miƙa fasfo ɗinsa.
Asali: Legit.ng


