Matasa Sun Fito daga Gidan Gwamnati, Sun Yi Wa Mata Masu Zanga Zanga Dukan Tsiya

Matasa Sun Fito daga Gidan Gwamnati, Sun Yi Wa Mata Masu Zanga Zanga Dukan Tsiya

  • Wasu mata da suka gudanar da zanga-zanga a bakin gidan gwamnatin Kwara sun kwashi kashinsu a hannu
  • Matan daga Oke-Ode a karamar hukumar Ifelodun sun yi zanga-zangar lumana kan matsalar tsaro da sace-sacen mutane
  • Shaidu sun ce wasu mutane dauke da sanduna sun fito daga Gidan Gwamnati suna dukan matan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ilorin, Kwara – Zanga-zangar lumana da mata suka gudanar a karshen mako kan matsalar tsaro ya rikide zuwa tashin hankali.

Matan na neman daukin gaggawa kan matsalar tsaro a Oke-Ode, karamar hukumar Ifelodun ta Jihar Kwara.

Ana zargin matasa daga gidan gwamnati sun lakadawa mata masu zanga-zanga duka
Gwamna Abdulrahman Abdulrazak na jihar Kwara. Kwara State Government.
Source: Twitter

Matasa sun ci 'zarafin' mata masu zanga-zanga

Daily Trust ta ruwaito cewa matan sun taru ne domin jan hankalin gwamnati kan hare-haren ‘yan ta’adda.

Sun koka kan ci gaba da tsare mazajensu da ‘ya’yansu da masu garkuwa da mutane ke yi na tsawon lokaci.

Kara karanta wannan

Mutane sun ga jirage na shawagi, sun fara guduwa saboda tsoron harin Amurka

Masu zanga-zangar sun bayyana cewa wadanda aka sace, ciki har da mazajensu, sun shafe watanni a hannun masu garkuwa da mutane ba tare da ganin wani gagarumin mataki daga gwamnati ba.

A yayin zanga-zangar, shaidu sun ce wani rukuni na maza dauke da sanduna sun fito daga cikin Gidan Gwamnati, inda suka fara dukan mata, lamarin da ya tilasta musu tserewa domin tsira da rayukansu.

Bidiyoyin ya bazu a kafafen sada zumunta wanda ya nuna yadda ake bulala da fatattakar matan, yayin da suke ihu suna neman taimako.

Wasu shaidu sun kuma zargi ‘yan sanda da ke wurin da kasa shiga tsakani domin dakile harin.

A cikin wani bidiyo, an ji wata mata tana cewa:

“Don Allah a taimake mu, muna cikin halin wahala game da ayyukan masu garkuwa da mutane a Oke-Ode.”

Harin ya haifar da martani da Allah-wadai daga mazauna jihar da kungiyoyin fararen hula.

A ranar Litinin 29 ga watan Disambar 2025, shugabannin adawa yayin wani hira da yan jaridu sun yi tir da lamarin.

Sun bayyana abin da ya faru a matsayin “cin zarafin tsofaffin mata” da suka fito zanga-zangar lumana domin jan hankalin gwamnati kan matsalar tsaro a yankunansu.

Kara karanta wannan

Daga tafiya daurin aure, mutane 7 'yan gari daya sun mutu a jihar Gombe

Sun kuma yi zargin cewa ‘yan daba na jam’iyyar APC ne aka sako wa matan domin cin zarafinsu.

Gwamna ya karyata hannu a cin zarafin masu zanga-zanga
Taswirar jihar Kwara da aka yi zanga-zanga a kofar gidan gwamnati. Hoto: Legit.
Source: Original

Martanin gwamnan Kwara kan dukan masu zanga-zanga

Sai dai a martaninsa ta shafin gwamnatin jihar na Facebook, Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya musanta duk wani hannu da gwamnatinsa ke da shi a harin.

Gwamnan ya bayyana abin da ya faru a matsayin abin da ba za a amince da shi ba, yana mai cewa lamarin ya sabawa ka’idoji da manufofin gwamnatinsa.

Gwamnan Kwara ya gargadi yan ta'adda

Mun ba ku labarin cewa gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq ya halarci bikin yaye sababbin jami'an tsaron dazuka da aka horas.

Abdulrahman Abdulrazaq ya yabawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu wajen kawo shirin samar da jami'an domin tunkarar matsalar rashin tsaro.

Hakazalika, ya aika da sakon gargadi ga 'yan ta'adda da masu garkuwa da mutane wadanda ke addabar jihar Kwara.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.