Kirsimeti: Gwamna Zulum Ya Gwangwaje Al'ummar Kiristoci a Borno

Kirsimeti: Gwamna Zulum Ya Gwangwaje Al'ummar Kiristoci a Borno

  • Al'ummar Kiristoci na ci gaba da shirye-shiryen gudanar da bukukuwan Kirsimeti na shekarar 2025 wadda ta zo karshe
  • Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya ba da kayan tallafi ga zawarawa da marasa galihu cikin al'ummar Kiristoci
  • Hakazalika ya kuma amince da tsarin kai Kiristoci wadanda ba 'yan asalin jihar Borno ba zuwa garuruwansu kyauta a mota

​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Borno - Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya raba kayan abinci masu muhimmanci ga al'ummar Kirista.

Gwamna Zulum ya raba kayayyakin ne ga zawarawa da kuma marasa galihu daga al’ummar Kirista, domin shirye-shiryen bikin Kirsimeti mai zuwa.

Gwamna Zulum ya raba kayan tallafi
Gwamna Babagana Zulum na raba kayan tallafi Hoto: Dauda Iliya
Source: Facebook

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Borno, Dauda Iliya ya sanya a shafinsa na Facebook.

Dauda Iliya ya ce Gwamna Zulum ya jagoranci rabon kayan tallafin a ranar Litinin, 22 ga watan Disamban 2025.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun yi aika aika bayan kai wani harin ta'addanci a Zamfara

Zulum ya ba da tallafi don Kirsimeti

Kowanne daga cikin waɗanda suka ci gajiyar tallafin, sama da mutane 6,000, ciki har da ’yan gudun hijira 1,605, ya samu buhun shinkafa guda ɗaya, kwali ɗaya na taliya da kuma galan ɗaya na man girki.

A cewar Zulum, wannan rabon daga cikin tallafin da yake bayarwa a kowace shekara ga Kiristoci domin rage musu dawainiya tare da tabbatar da cewa sun yi bikin Kirsimeti cikin farin ciki da mutunci.

Gwamnan ya kuma amince da sufuri kyauta ga Kiristocin da ba ’yan asalin Borno ba, domin su tafi zuwa garuruwansu na asali yayin bukukuwan.

Gwamna Zulum ya yi nasiha

Zulum ya jaddada muhimmancin zaman lafiya, haɗin kai da bunkasa tattalin arziki tare a tsakanin dukkan al’ummar jihar Borno, ba tare da la’akari da bambancin addini ko ƙabila ba.

"Fatan da na ke da shi a zuciyata shi ne dangantakar da ta daɗe tsakanin Musulmi da Kiristoci a jihar Borno ta ci gaba da dorewa."

Kara karanta wannan

APC ta yi babban rashi, jigonta kuma tsohon kwamishina yar bar duniya

"Ina roƙon Allah Maɗaukakin Sarki, cikin rahamarsa marar iyaka, Ya albarkaci al’ummominmu, Ya kuma tabbatar da zaman lafiya da jituwa tsakanin addinan biyu.”
"Koyarwar Musulunci ta fayyace cewa Musulmi suna buƙatar zaman tare cikin lumana da waɗanda ba Musulmi ba, kamar yadda Alƙur’ani ya koyar, kuma na yi imanin cewa akwai hakan a cikin littafin Kirista”

- Gwamna Babagana Umara Zulum

Zulum ya ba Kiristoci kayan abinci
Kayan abincin da Gwamna Zulum ya rabawa Kiristoci Hoto: Dauda Iliya
Source: Facebook

Gwamnan Borno, Zulum ya samu yabo

Shugaban kungiyar Kiristoci ta CAN a jihar Borno, Rabaran John Bogna Bakeni, wanda ya tarbi gwamnan, ya nuna godiya mai yawa bisa ci gaba da nuna tausayi da tallafin da yake bayarwa.

"Muna miƙa godiyarmu gare ka, Mai Girma Gwamna. Wannan abu yana da matukar muhimmanci a gare mu, al’ummar Kirista a jihar Borno."

- Rabaran John Bogna Bakeni

Gwamnati ta ba da hutun Kirsimeti

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnatin tarayya ta ba da hutu domin bukukuwan Kirsimeti na shekarar 2025.

Ministan harkokin cikin gida Dr. Olubunmi Tunji-Ojo ya ayyana ranakun Alhamis, 25 da Jumma'a 26 ga watan Disamban 2025 a matsayin ranakun hutu.

Hakazalika ya bayyana ranar da za a yi hutu domin murnar shigowar sabuwar shekara ta 2026 da ke shirin kamawa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng