Ana Wata ga Wata: An Hango Jirgin Leken Asirin Amurka Yana Shawagi a Najeriya

Ana Wata ga Wata: An Hango Jirgin Leken Asirin Amurka Yana Shawagi a Najeriya

  • Tun daga Nuwamba, 2025 ne aka rahoto cewa wasu jiragen leken asirin kasar Amurka na yin shawagi a sararin samaniyar Najeriya
  • Rahotanni sun danganta hakan da barazanar daukar matakin sojoji da shugaban Amurka, Donald Trump ya yi a kwanakin baya
  • Jiragen na tattara bayanai kan Boko Haram da ISWAP tare da bin sawun wasu masu garkuwa da mutane don sanin maboyarsu

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Borno - Rahotanni sun nuna cewa Amurka ta fara tura jiragen leken asiri a manyan sassan Najeriya tun daga karshen watan Nuwamba, 2025.

Rahoton na musamman da aka fitar a ranar Litinin, bisa bayanan bin diddigin jirage da kuma majiyoyin gwamnatin Amurka, ya ce ba a iya tabbatar da ainihin manufar ayyukan wadannan jirage ba.

Amurka na ci gaba da tattara bayanai kan 'yan ta'adda ta hanyar tura jiragen leken asiri Najeriya.
Yadda wani jirgin leken asirin Amurka ya rika shawagi a wasu jihohin Arewa maso Gabashin Najeriya. Hoto: @BrantPhilip_, @usairforce
Source: Twitter

Kamfanin jaridar Rauters ya rahoto cewa wannan mataki na zuwa ne bayan barazanar da shugaban Amurka Donald Trump ya yi wa Najeriya a watan Nuwamba, 2025.

Kara karanta wannan

Kasar Amurka ta yanke matsaya game da maganar turo dakarun sojoji Najeriya

A lokacin, ya yi baraanar daukar matakin soji a Najeriya saboda abin da ya bayyana a matsayin gazawar gwamnati wajen dakile hare-haren da ake kai wa al’ummomin Kirista.

Haka kuma, ayyukan leken asirin sun zo ne bayan sace wani matukin jirgin Amurka da ke aiki da wata kungiyar yada addini a kasar Nijar a watannin baya.

Bayanan bin diddigin jirage na watan Disamba, 2025 sun nuna cewa jiragen da ke gudanar da aikin yawanci, suna tashi daga Ghana, suna shawagi a sararin samaniyar Najeriya, sannan su koma Accra, babban birnin Ghana.

An gano cewa kamfanin da ke sarrafa jiragen shi ne Tenax Aerospace, wani kamfani da ke jihar Mississippi a Amurka, wanda ke samar da jiragen ayyuka na musamman kuma ke aiki kafada da kafada da sojojin Amurka.

Sai dai kamfanin bai amsa bukatar jin ta bakinsa ba, kamar yadda jaridar Vanguard ta rahoto.

Ghana: Cibiyar aikin sojin Amurka

Shugaban tawagar Afirka da ke kula da muhimman ayyuka a cibiyar Amurka (AEI), Liam Karr, wanda ya yi nazari kan bayanan jiragen, ya ce alamu na nuna ana gudanar da aikin ne daga Accra.

Kara karanta wannan

Wata sabuwa: Donald Trump ya janye jakadan kasar Amurka daga Najeriya

A cewar Liam Karr, Accra sananniya ce a matsayin cibiyar dabaru da kayayyakin aiki ta sojojin Amurka a Afirka, in ji rahoton Punch.

Liam Karr ya ce wannan na iya nuna cewa Amurka na sake gina karfin leken asirinta a yankin, musamman bayan da Nijar ta kori sojojin Amurka daga wani muhimmin sansanin jiragen sama a hamada, tare da karkata ga Rasha domin taimakon tsaro.

Wasu jami'an tsaro a Amurka sun tabbatar da jirgin kasarsu na shawagin tattara bayanan sirri a Najeriya.
Wani jirgin saman Amurka da dalibin koyon tuka jirgin sojojin sama ke sarrafawa. Hoto: @usairforce
Source: Twitter

Mayar da hankali kan Boko Haram da ISWAP

Wani tsohon jami’in Amurka ya bayyana cewa jirgin na daga cikin wasu kadarorin tsaro da gwamnatin Trump ta mayar da su Ghana a watan Nuwamba.

Ya ce ayyukan jirgin sun hada da; bin sawun matukin jirgin Amurka da aka sace, tattara bayanai kan kungiyoyin ‘yan ta’adda a Najeriya, ciki har da Boko Haram da ISWAP.

Wani jami’in gwamnati na yanzu ya tabbatar da cewa jirgin na shawagi a sararin samaniyar Najeriya, amma ya ki bayar da cikakken bayani saboda dalilan diflomasiyya.

Najeriya da Amurka sun yi sasanci

A wani labarin, mun ruwaito cewa, gwamnatin tarayya ta bayyana cewa rikicin diflomasiyya da ya taso tsakaninta da Amurka ya lafa matuka bayan doguwar tattaunawa.

Kara karanta wannan

Rundunar sojojin sama ta biya diyya ga iyalan bayin Allah da ta kashe a Sokoto

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin wani taron manema labarai na karshen shekara da aka gudanar a Abuja.

Ministan ya ce rikicin ya biyo bayan kalaman shugaban Amurka, Donald Trump, inda ya zargi Najeriya da yi wa Kiristoci kisan gilla tare da yin barazanar daukar matakin soji.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com