Jerin Mutane, Kungiyoyi 31 da Tinubu Zai Ayyana Yan Ta’adda a Sabon Tsarin Tsaro

Jerin Mutane, Kungiyoyi 31 da Tinubu Zai Ayyana Yan Ta’adda a Sabon Tsarin Tsaro

  • Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da sabon tsari na yaƙi da ta’addanci a Najeriya baki daya
  • Tinubu zai ayyana ’yan bindiga, masu garkuwa, masu karɓar kuɗin fansa da masu taimaka musu a matsayin ’yan ta’adda
  • Shugaban ya ce manufar ita ce kare zaman lafiyar ƙasa, rage fargabar jama’a da tabbatar da sakamako mai gamsarwa daga kuɗaɗen tsaro

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Tsaron Najeriya ya shiga sabon salo bayan da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da sabuwar manufar yaƙi da ta’addanci.

Sabon tsarin ya sake fayyace waɗanda za a ɗauka a matsayin ’yan ta’adda a ƙarƙashin dokar ƙasa.

Mutane da kungiyoyi da za a ayyan yan ta'adda a Najeriya
Ministan tsaro a Najeriya, Christopher Musa da gungun yan ta'adda. Hoto: Christopher Musa/x.
Source: Twitter

Sabon tsarin tsaron Tinubu a Najeriya

A sabon umarnin, gwamnatin tarayya ta ayyana ƙungiyoyin ɗauke da makamai, masu garkuwa da mutane, masu karɓar kuɗin gayya, da duk masu ba su taimako a matsayin ’yan ta’adda, cewar Punch.

Kara karanta wannan

'Babu tausayi': Tinubu ya kuma yin albishir ga 'yan Najeriya game da ta'addanci

Shugaba Tinubu ya bayyana hakan ne a cikin jawabin kasafin kuɗin ƙasa, inda ya ce gwamnati na zuba jari a harkar tsaro.

Ya jaddada cewa sabon tsarin zai sauya gaba ɗaya yadda Najeriya ke fuskantar ta’addanci da laifuka masu amfani da makamai.

Ya ce masu garkuwa da fararen hula da ƙungiyoyin da ke tilasta wa al’umma biyan kuɗi za a yi musu hukunci a matsayin ’yan ta’adda.

Haka kuma, duk wanda ya mamaye ko ya yi yunƙurin mamaye wani yanki na ƙasar Najeriya ta hanyar amfani da ƙarfi, zai fuskanci wannan hukunci.

Tinubu yana daukar matakai domin kakkabe ta'addanci
Shugaba Bola Tinubu yayin jawabi a Abuja. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Facebook

Mutane, kungiyoyi da za a ayyana yan ta'adda

Wani masanin harkokin tsaro a Najeria ya wallafa jerin wadanda za su iya shiga cikin yan ta'addan a kasar.

Matashin ya wallafa haka a shafinsa na X inda ya ce a sabon tsarin, za a saka su cikin yan ta'adda a Najeriya.

A sabon tsarin, mutanen sun haɗa da:

  1. Ƙungiyoyin da ke ɗauke da makamai ba tare da ikon gwamnati ba
  2. Mutanen da ke amfani da makamai masu hatsari ba tare da izini ba
  3. ’Yan bindiga
  4. Mayaƙan sa-kai (militias)
  5. Ƙungiyoyin ’yan daba masu makamai
  6. Ƙungiyoyi masu amfani da makamai
  7. ’Yan fashi da makami
  8. Ƙungiyoyin asiri
  9. Ƙungiyoyin ’yan bindiga da ke zaune a dazuka
  10. Sojojin haya masu alaƙa da ƙasashen waje
  11. Masu tayar da hankali a siyasa
  12. Masu tayar da rikicin ƙabilanci
  13. Masu aikata tashin hankali don kuɗi
  14. Masu tayar da rikicin addini
  15. Masu garkuwa da mutane
  16. Masu tilasta karɓar kuɗi
  17. Masu ɗaukar nauyin ƙungiyoyin makamai
  18. Masu sarrafa kuɗaɗen ƙungiyoyin ta’addanci
  19. Masu ɓoye ’yan ta’adda
  20. Masu ba da bayanan sirri (’yan leƙen asiri)
  21. Masu taimakawa biyan kuɗin fansa
  22. Masu shiga tsakani wajen tattaunawar kuɗin fansa
  23. ’Yan siyasar da ke kare ’yan ta’adda
  24. ’Yan siyasar da ke shiga tsakani don kare ayyukan tashin hankali
  25. Masu jigilar mayaƙa ko makamai
  26. Masu sayar da makamai
  27. Masu ba da mafaka
  28. ’Yan siyasar da ke ƙarfafa tashin hankali
  29. Sarakunan gargajiya da ke tallafa wa ta’addanci
  30. Shugabannin al’umma da ke taimaka wa tashin hankali
  31. Shugabannin addini da ke kare ko halasta ta’addanci.

Kara karanta wannan

Bayan takunkumin Amurka, Trump ya kara saka doka ga 'yan Najeriya da wasu kasashe

Tinubu ya sha alwashin kakkabe yan ta'adda

Mun ba ku labarin cewa shugaba Bola Tinubu ya sha alwashin ci gaba da yaki da ta'addanci domin tabbatar da samun zaman lafiya.

Tinubu ya nuna cewa babu sassauci ga ’yan ta’adda, ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane a fadin kasar.

Shugaban ya ce gwamnati za ta tabbatar da daidaiton tattalin arziki da tsaro mai ɗorewa a Najeriya baki daya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.