Tawagar Amurka Ta Dauki Jiha 1 a Arewa, Ta Kawo Ziyara kan Zargin Kisan Kiristoci a Najeriya

Tawagar Amurka Ta Dauki Jiha 1 a Arewa, Ta Kawo Ziyara kan Zargin Kisan Kiristoci a Najeriya

  • Tawagar 'yan Majalisar Amurka ta kai ziyara jihar Benuwai a wani mataki na bincike kan zargin yi wa kiristoci kisan kare dangi a Najeriya
  • Gwamna Hyacinth Alia ya karbi tawagar a gidan gwamnatinsa da ke birnin Makurdi, kuma sun tattauna kafin su kai ziyara wata coci
  • Dan majalisa Riley M. Moore ya ce sun gana da Bishof Wilfred Anagbe, Bishop Isaac Dugu da Mai Martaba Sarkin kabilar Tiv, James Ioruza

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Benue, Nigeria - Wata tawaga ta ’yan majalisar dokokin Amurka da sauran jakadu ta kawo ziyara Najeriya domin bincike kan zargin yiwa kiristoci kisan kare dangi a kasar.

Wannan tawaga ta Amurka ta wuce zuwa jihar Benuwai domin gano gaskiyar abin da ke faruwa kan zargin da ake yi na kokarin karar da kiristoci.

Kara karanta wannan

Zargin kisan kiristoci: Amurka da Najeriya sun fara samun fahimtar juna

Gwamnan jihar Benuwai, Hyacinth Lormem Alia.
Gwamna Hyacinth Alia a fadar gwamnatin Benuwai da ke Makurdi Hoto: Rv. Fr. Hyacinth Lormem Alia
Source: Facebook

Gwamna Hyacinth Alia na jihar Benuwai ya tabbatar da ziyarar 'yan Majalisar Amurka a wata sanarwa da ya fitar, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tawagar Amurka ta gana da Gwamna Alia

Gwamna Alia ya karɓe su a Birnin Makurdi ranar Asabar, inda suka yi wata ganawa ta sirri a cikin Gidan Gwamnati.

A wata sanarwa da gwamnan ya fitar bayan ganawa da tawagar 'yan Majalisar Amurka, Alia ya ce:

“Mun tattauna ne kan batutuwan tsaro da na jin kai da ke addabar jihar Benuwai da Arewa ta Tsakiya, da bukatar kawo zaman lafiya mai ɗorewa, adalci da tsaro ga mutanenmu.”

Daga baya tawagar ta kuma ziyarci Cocin Katolika da ke kusa da Gidan Gwamnati, inda suka sake wata ganawa ta sirri da Bishof Wilfred Anagbe na majami'ar Maki da wasu manyan limamai.

'Yan Majalisar Amurka da suka shigo Najeriya

Tawagar 'yan Majalisar dokokin Amurka ta ƙunshi, Mario Díaz-Balart, Norma Torres, Scott Franklin, Juan Ciscomani, Riley M. Moore da Jakadan Amurka a Najeriya, Richard Mills.

Kara karanta wannan

Gwamnoni 19 za su tara Naira biliyan 19 duk wata, an jero abubuwan da za su yi a Arewa

Dan Majalisa Moore ya tabbatar da ganawar a shafinsa na X, inda ya ce:

"Girmamawa ne da muka samu damar ganawa da Bishof Wilfred Anagbe, Bishof Isaac Dugu da Mai Martaba James Ioruza, Sarkin al’ummar Tiv.”
Tawagar Amurka.
Dan majalisar Amurka, Riley Moore tare da wasu malaman coci da Sarkin Tiv a jihar Benuwai Hoto: @RepRileyMoore
Source: Twitter

Ribadu ya gana da tawagar Amurka

Lafin su tafi jihar Benuwai, tawagar ta gana da Mai Bada Shawara Kan Harkokin Tsaro (NSA), Nuhu Ribadu, a Abuja.

Wannan ganawar ta mayar da hankali ne kan batun yaƙi da ta’addanci, tsaron yankin Arewa da Sahel da karfafa dangantakar tsaro tsakanin Najeriya da Amurka

Ribadu ya bayyana cewa tattaunawar ta ƙara gina aminci da haɗin kai tsakanin ƙasashen biyu, tare da fatan hakan zai taimaka wajen kawo zaman lafiya da tsaro mai ɗorewa.

Bulama ya ba tawagar Amurka shawara

A wani rahoton, kun ji cewa fitaccen mai sharhi kan tsaro, kuma dan fafutukar kare hakkin dan adam, Barista Bulama Bukarti, ya yaba da ziyarar tawagar Amurka zuwa Najeriya.

Bukarti ya jaddada cewa tawagar ta gane wa idanunta yadda 'yan Najeriya ke rayuwa zai fi zama maifi dacewa a kan ta yi amfani da maganganun siyasa kawai.

Kara karanta wannan

Bulama Bukarti ya bada shawara bayan shigowar tawagar Amurka Najeriya

Ya bada shawarar cewa ya kamata wannna tawaga ta yan Majalisar Amurka ta fadada ziyararta zuwa jihohin Arewa musamman wadanda ke fama da matsalar tsaro.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262