Tinubu Ya Yi Maraba da Ceto Daliban Neja, Ya Ba Jami'an Tsaro Sabon Umarni

Tinubu Ya Yi Maraba da Ceto Daliban Neja, Ya Ba Jami'an Tsaro Sabon Umarni

  • Wasu daga cikin daliban da 'yan bindiga suka sace a jihar Neja sun shaki iskar 'yanci bayan sun kwashe kwanaki a hannun tsageru
  • Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yabawa jami'an tsaro bisa kokarin da suka yi wajen kubutar da daliban wadanda aka sace cikin dare a makaranta
  • Mai girma Bola Tinubu ya kuma taya gwamnan jihar Neja, Umaru Bago, murnar ganin yaran sun dawo cikin koshin lafiya

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi martani bagan ceto dalibai 100 daga cikin wadanda 'yan bindiga suka sace a Neja..

Shugaba Tinubu ya yaba wa hukumomin tsaro bisa kokarin da suka yi wajen kubutar da dalibai 100 na makarantar Katolika da aka kai wa hari a jihar Neja.

Tinubu ya yi murna da ceto daliban Neja
Daliban Neja da aka ceto da Shugaba Bola Tinubu Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai ba Shugaba Tinubu shawara kan harkokin yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar a shafinsa na X, a ranar Litinin, 8 ga watan Disamban 2025.

Kara karanta wannan

Gwamna Fubara ya sa labule da Tinubu bayan ficewar 'yan majalisa zuwa APC

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu ya ba jami'an tsaro umarni

Yayin da yake nuna farin cikinsa kan dawowar daliban, Shugaba Tinubu ya umarci hukumomin tsaro da su hanzarta ceto sauran dalibai 115 da malamansu da har yanzu suke tsare a hannun ’yan bindiga.

A cewar Bayo Onanuga, Shugaba Tinubu ya tabbatar wa iyayen daliban cewa gwamnatin tarayya da ta jihar Neja na aiki tare domin ganin an mayar da dukkan yaran gidajensu lafiya.

“An ba ni rahoton dawowar dalibai 100 na makarantar Katolika da ke jihar Neja. Ina taya Gwamna Umar Bago farin ciki, kuma ina yabawa jami’an tsaro bisa jajircewarsu wajen ganin an dawo da yaran tun bayan harin da aka kai ranar 21 ga Nuwamba."

- Shugaba Bola Tinubu

Shugaban kasar ya ce umarninsa ga jami’an tsaro bai sauya ba kan ceto daliban da aka sace.

“Dole ne dukkan daliban da sauran ’yan Najeriya da aka yi garkuwa da su a fadin kasa a ceto su, a dawo da su gida lafiya. Sai mun tabbatar da an samo su gaba ɗaya."

Kara karanta wannan

Gwamnati ta cika alkawari, ta ceto daliban makarantar Neja 100 daga ƴan ta'adda

- Shugaba Bola Tinubu

Gwamnatin Tinubu za ta kula da tsaro

Ya kara da cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da aiki tare da jihar Neja da sauran jihohi domin tsare makarantu a kasar nan da kuma tabbatar da ingantaccen tsaro ga ɗalibai.

Shugaba Tinubu ya umarci a ceto ragowar daliban da aka sace a Neja
Shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu Hoto: @aonanuga1956
Source: Facebook
“Daga yanzu, dole ne hukumomin tsaro tare da hadin guiwar gwamnonin jihohi su dakile duk wani yunkurin sace dalibai nan gaba."
"Ba za mu yarda yaranmu su ci gaba da zama kamar ganima a gaban ’yan ta’adda marasa tausayin da ke neman dakile iliminsu da jefa su da iyayensu cikin tashin hankali ba.”

- Shugaba Bola Tinubu

Shugaba Tinubu ya gana da Gwamna Fubara

A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya karbi bakuncin gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara.

Mai girma Bola Tinubu ya gana da Gwamna Fubara ne a fadar shugaban kasa ta Aso Rock Villa da ke babban birnin tarayya Abuja.

Kara karanta wannan

Matan da Shugaba Tinubu ya zaba don zama jakadun Najeriya a kasashen waje

Ganawar ta su dai na zuwa ne bayan mafi yawa daga cikin 'yan majalisar dokokin jihar Rivers sun sauya sheka daga jam'iyyar PDP zuwa APC.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng