Ya Matso Kusa da Najeriya: Sojoji Sun Sake Juyin Mulki a Afrika ta Yamma

Ya Matso Kusa da Najeriya: Sojoji Sun Sake Juyin Mulki a Afrika ta Yamma

  • Ana fargabar sojoji sun sake yin juyin mulki a wata kasar Afirka bayan kifar da gwamnatin Guinea-Bissau a kwanakin baya
  • Majiyoyi sun ce sojoji sun bayyana a gidan talabijin na Benin inda suka sanar da rushe gwamnatin kasar ba tare da bata lokaci ba
  • Alamu sun nuna wannan juyin mulki ne da ya kifar da Shugaba Patrice Talon wanda ke da makwabtaka da kasar Najeriya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Porto-Novo, Benin - Wani rukuni na sojoji sun bayyana a gidan talabijin na gwamnati a Jamhuriyar Benin, inda suka sanar da rushe gwamnati.

Wannan lamari da ake ganin na kama da juyin mulki ya tayar da hankula ganin yadda rushe dimokuraɗiyya ke kara yawa.

An kwace ikon gwamnati a Benin
Shugaba Patrice Talon da aka kifar da gwamnatinsa. Hoto: EVARISTO SA.
Source: Getty Images

Sojoji sun karbi iko a Jamhuriyar Benin

Rahoton Aljazeera ya tabbatar da cewa sojojin sun sanar hakan ne a ranar Lahadi 7 ga watan Disambar 2025.

Kara karanta wannan

An buga rikici da Matawalle a ma'aikatar tsaro kafin Badaru ya ajiye aiki

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sun bayyana cewa sun hambarar da Shugaba Patrice Talon, wanda yake mulki tun shekarar 2016, lamarin da ya tada hankulan jama’a.

Ana jiran ƙarin bayani kan wannan sabon juyin mulki, yayin da lamarin ya jefa al’ummar ƙasar cikin fargaba da rashin tabbas game da makomar Benin.

Ana fargabar an kwace mulki a Benin
Shugaba Patrice Talon da aka ce an yi wa juyin mulki. Hoto: Patrice Talon.
Source: Facebook

Bayanai kan yadda tashin hankalin ya fara

A cewar France24, tashin hankalin ya fara ne da sassafe lokacin da aka kai hukumar harin makami a gidan shugaban ƙasa Patrice Talon da ke Porto-Novo.

Rahotanni sun ce Laftanar-Kanal Pascal Tigri ne ya jagoranci harin, tare da sojojin da ke biyayya gare shi, inda daga baya suka kwace ikon gidan talabijin na ƙasa.

Bidiyon da aka nuna a talabijin na gwamnati ya nuna sojoji cikin kayansu suna karanta sanarwa, suna ikirarin cewa sun ɗauki mulki ne “don dawo da oda”.

Babu inda aka samu labarin inda Talon ya ke a lokacin, sai dai Ofishin Jakadancin Faransa ya ce an ji karar harbe-harbe a sansanin "Guezo” kusa da wurin zaman shugaban ƙasa.

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun kutsa gidan malamin addini a Kaduna da dare, sun sace shi

Gargadin Faransa ta yi wa yan kasarta

Ofishin ya shawarci ‘yan ƙasar Faransa da su zauna a cikin gidajensu saboda tsaro har zuwa lokacin da lamura za su dawo daidai kamar yadda suke a baya.

Benin, wacce ake kira Jamhuriyar Benin tsohuwar Masarautar Dahomey, ƙasa ce a Yammacin Afirka da ke iyaka da Togo a Yamma.

Har ila yau, tana da kusanci da NajeriyaGta gabas, Burkina Faso a arewa maso Yamma, sannan Niger a Arewa maso Gabas.

An yi juyin mulki a Guinea-Bissau

A baya, kun ji cewa sojojin Guinea-Bissau sun sanar da cewa sun karɓi cikakken iko a ƙasar bayan kwanaki uku kacal da zaɓen ’yan majalisa da na shugaban ƙasa.

Rahotanni sun nuna cewa tun da safiyar ranar Laraba 26 ga watan Nuwambar 2025, aka ji karar harbe-harbe a kusa da fadar shugaban ƙasa, sojoji sun mamaye manyan hanyoyi.

Dakarun sojin sun karanta sanarwa daga Babban Hedikwatar Soji a Bissau, babban birnin kasar bayan sun gama kwace iko da kuma kama shugaban kasa.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.