'Yan Ta'adda Sun Yankawa Manoman Zamfara Harajin Girbi

'Yan Ta'adda Sun Yankawa Manoman Zamfara Harajin Girbi

  • Al’ummomin karkara a Bungudu sun ce ’yan bindiga suna tilasta wa manoma biyan haraji mai tsauri kafin su girbe amfanin gona
  • Rahotanni sun nuna cewa Durkai, Honkarhe, Makwa da Kiluta suna daga cikin waɗanda ƴan ta'adda suka umarta da su biya miliyoyin Naira
  • 'Yan bindigan suna ci gaba da jefa rayuwar jama'a a cikin rashin tabbas, sannan suna kara tsoratar da jama'a da barazanar hari

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Zamfara – Al’ummomin karkara da ke cikin Karamar Hukumar Bungudu a Jihar Zamfara sun sake tashi da wata sabuwar matsala saboda ƴan ta'adda.

Rahotanni sun iske jama'a na cewa nuna ’yan bindiga sun ƙara matsa lamba tare da kakaba haraji mai nauyi kan manoma da ke son girbe amfanin bana.

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun kashe mutane saboda 'Rufaida yoghurt' a Zamfara

Yan ta'adda sun sako mazauna Zamfara a gaba
Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara Hoto: Dauda Lawal
Source: Twitter

Mai sharhi a kan harkokin tsaro a yankin Arewa maso Yamma, Bakatsine, ne ya wallafa hakan a shafinsa na X a ranar Juma’a.

Ƴan ta'adda sun sako Zamfarawa a gaba

Rahoton ya ce wadanda abin ya shafa sun ce a yanzu ba a bari manoma su kusanci gonakinsu sai sun biya kudin da ’yan bindigan suka ce dole sai an biya.

Al’ummomin Durkai, Honkarhe, Makwa da Kiluta ne suka fi fuskantar wannan matsin lamba, inda ake zargin cewa sun ɗorawa kowane yanki kuɗin da ya zarta ƙarfin jama’ar da ke zaune a can.

Wani mazaunin yankin ya shaida cewa,:

"Manoma a Durkai, Honkarhe, Makwa da Kiluta since an ɗora masu harajin girbi mai nauyi kafin su ciro amfanin gonakinsu."

Harajin da ƴan ta'adda suka dora a Zamfara

Ƴan ta'adda sun dora wa kowane manomi a Durkai da Honkarhe harajin girbi da ya kai N5m.

Kara karanta wannan

Sheikh Gumi ya yi zazzafar addu'a kan 'yan ta'adda da masu taimakonsu

Makwa kuwa an ce an umurce su da su biya wani adadi mai kauri, yayin da Kiluta ma ta sami irin wannan harajin na N5m.

Yan ta'adda sun ɗorawa mazauna Zamfara haraji
Wasu yan ta'adda da suka addabi jama'a a Najeriya Hoto: @ZagazOlaMakama
Source: Twitter

Wadannan buƙatu sun saka jama’ar yankunan cikin fargaba da tashin hankali, musamman ganin cewa manoma su ne ginshiƙan tattalin arzikin yankin.

Rahotannin sun ƙara bayyana cewa lamarin ya kai wani mataki mai ban tsoro, inda ake zargin ’yan bindigan sun fara sa farashin kayayyaki, musamman babura.

Mutane a yankin sun ce farashin babur ɗin Honda ya kai kusan N1.7m saboda tsoma bakin ’yan ta’addan a kasuwa.

Ƴan jarida sun shiga damuwa kan tsaro

Kungiyar yan jarida masu kishin zaman lafiya ta Kano KCJF ta bayyana takaici a kan yadda tsaro ya zama abin siyasantar wa a Arewacin Najeriya.

Kungiyar ta bakin Shugabarta Aisha Ahmad ta ce jihohi irinsu Zamfara da ake siyasantar da batun tsaro yana kara dagula al'amura.

Kungiyar ta ce:

"Wannan ya zargi wannan, wancan ya ce kazaa duk yana taimakawa ƴan ta'adda su ci karensu babu babbaka."
"Irin wannan haraji da ƴan ta'adda ke dorawa mutane zai sa jama'a su koma gare su neman mafita ba gwamnati ba."

Kara karanta wannan

Tashin hankali: 'Yan bindiga sun kai mummunan hari garuruwan Fulani 4 a Kaduna

Ƴan bindiga sun kai hari a Zamfara

A baya, kun ji cewa 'yan bindiga sun kai hari a ƙauyen Danjibga da ke ƙaramin hukumar Tsafe a Zamfara, bayan takaddama kan madarar Rufaida Yoghurt da ake sayarwa a cikin ƙauyen.

Mazauna ƙauyen sun ce ƴan ta'addan sun je shagon sayar da yoghurt don saya — amma suka dauka ba tare da biyan kudi ba, lamarin da mai shagon ya ce ba zai lamunta ba.

Daga ƙarshe suka bar yoghurt ɗin a waje suka tafi. Bayan ƙasa da sa’a guda, ‘yan bindigar suka dawo da makamai, suka fara harbe-harbe a cikin ƙauyen tare da kashe mutane.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng