Shugaban Karamar Hukumar da Ke Fama da Rashin Tsaro Ya Raba Motoci ga Kansiloli

Shugaban Karamar Hukumar da Ke Fama da Rashin Tsaro Ya Raba Motoci ga Kansiloli

  • Shugaban Karamar Hukuma ya tallafawa al'ummarsa domin tsayawa da ƙafafunsu a Katsina da ke fama da matsalolin tsaro
  • Hon. Abdullahi Sani wanda ke jagorantar karamar hukumar Safana shi ya yi wannan abin alheri wanda ya samu yabo daga gwamna
  • Safana na daga cikin ƙananan hukumomi da ke fama da matsalolin tsaro a jihar musamman daga yan bindiga

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Safana, Katsina - Shugaban Karamar Hukuma a jihar Katsina ya yi abin a yaba ga al'ummar yankinsa domin dogaro da kansu.

Shugaban karamar hukumar Safana a Jihar, Alhaji Abdullahi Sani, ya tallafawa mutane 1,322 a yankinsa.

A raba motoci ga kansiloli a Katsina
Gwamna Dikko Umaru Radda na Katsina. Hoto: Dr. Dikko Umaru Rassa.
Source: Facebook

An raba motoci ga kansiloli a Katsina

Rahoton Punch ya ce Hon. Sani ya kuma raba motoci 10 ga kansiloli a karamar hukumarsa domin morar romon dimokuraɗiyya.

Kara karanta wannan

Karancin abinci: Manoma 14,000 sun samu tallafin N4bn a jihar Bauchi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majiyoyi sun bayyana cewa Gwamna Dikko Radda ne ya kaddamar da shirin a Safana cikin wani taron karfafawa al’ummar yankin guiwa.

Radda ya yaba wa shugaban kananan hukumomin, yana kiran shirin “mafi inganci da karfafawa jama’a” cikin jerin yankunan da ya ziyarta.

Ya kuma jinjinawa shugaban Safana saboda nuna jagoranci nagari da ƙoƙarin inganta al'umma yana cewa hakan misali ne na kawo sauyi mai ɗorewa.

Gwamnan ya ce shirin ya tabbatar da yadda ‘yancin kananan hukumomi ke iya kawo ci gaba ga al’umma ta hanyar ayyuka kai tsaye ga talakawa.

Radda ya bayyana cewa shirin ya nuna yunkurin faɗaɗa kasuwanci, ƙarfafa dogaro da kai, da gina karfin tattalin arzikin al’ummomin Safana gaba ɗaya.

Ya ce:

“Wannan shi ne ainihin manufar ‘yancin kananan hukumomi: ci gaban da ke tasowa daga ƙasa yana inganta rayuwar mutane kai tsaye babu tsaiko.”
Gwamna Radda ya yabawa shugaban karamar hukuma a Katsina
Taswirar jihar Katsina da ke makwabtaka da Nijar. Hoto: Legit.
Source: Original

Gwamna Radda ya yabawa shugaban karamar hukuma

Radda ya kara da cewa shirin Safana shi ne mafi girma da ya gani tun farkon zagayen da yake yi, ya ce hakan na zama abin koyi ga sauran kananan hukumomi.

Kara karanta wannan

An kakaba dokar hana fita a Kogi bayan haramta dukkan bukukuwan addini

Gwamnatin jihar ta ce za ta ci gaba da ɗaukar matakan tallafawa matasa, mata da masu rauni ta hanyar ƙarfafa shirye-shiryen karfafawa al’umma a Katsina.

A nasa bangaren, shugaban ƙaramar hukumar ya gode wa gwamna saboda sakin kudaden da suka ba shi damar aiwatar da wannan gagarumin shirin.

Kayan da aka raba sun haɗa da injunan dinki, nika, babura, injin noma, mota ta musamman ga shugaban APC na yankin.

An kuma raba buhunan fulawa, kekuna ga masu nakasa, tallafin kuɗi ga mata, matasa, masu rauni, da shugabannin APC na ƙaramar hukuma da gundumomi.

Radda ya kuma yi rangadi a dukkan kananan hukumomi 34, tare da kai gaisuwa ga Sarkin Safana, Yariman Katsina Alhaji Sada Rufa’i a lokacin ziyarar.

Yan bindiga: Tsohon mataimakin ciyaman ya kubuta

An ji cewa a kwanakin baya 'yan bindiga suka yi awon gaba da tsohon mataimakin shugaban karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina.

Yan bindigan sun tsare Nasiru Abdullahi Dayi a hannunsu har na tsawon kwanaki 103 kafin ya shaki iskar 'yanci.

Iyalan dan siyasar sun bayyana halin da suka tsinci kansu a ciki a tsawon kwanakin da ya kwashe ba ya tare da su.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.