Barazanar 'Yan Bindiga: Gwamnatin Jihar Kano Ta Yi Magana kan 'Yan Acaba

Barazanar 'Yan Bindiga: Gwamnatin Jihar Kano Ta Yi Magana kan 'Yan Acaba

  • Gwamnatin Kano ta ce ta samu sahihan bayanan yaɗuwar masu acaba a wasu unguwanni duk da hana su da aka dade da yi
  • Ta ce jami’an tsaro suna samun cikakken goyon baya wajen ɗaukar matakai a kan matsalar rashin tsaro da ake samu a jihar
  • An fara nazarin shawarwarin jama’a kan ƙarin sa ido da tsauraran matakan tsaro a manyan hanyoyin shiga da fita daga jihar Kano

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Kano – Gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin Abba Kabir Yusuf ta bayyana cewa tana bibiyar korafe-korafen jama’a dangane da ƙara yaɗuwar sana’ar acaba a sassa daban-daban na Kano.

Mutane na korafi game da 'yan acaba ne bayan fara kai hare-hare da aka yi jihar a 'yan kwanakin nan.

Kara karanta wannan

Kano: Gwamnati ta yi bayani kan dokar hana acaba, an yi sassauci a wasu yankuna

Wasu 'yan acaba dauke da fasinja
Tarin 'yan acaba da suka fito bakin aiki a wata jiha. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Kwamishinan yada labaran jihar, Ibrahim Waiya ne ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X.

Magana kan 'yan acaba a Kano

Sanarwar ta ce akwai bayanai da suka nuna yadda acaba ke sake bayyana a unguwanni daban-daban a cikin Kano, duk da cewa wannan sana’a na daga cikin abubuwan da aka haramta a jihar.

An kuma samu rahotannin da ke nuna cewa wasu kananan hukumomi da ke iyaka da Kano na fuskantar irin wannan matsala.

Gwamnatin ta jaddada cewa wadannan bayanai sun sanya ta ɗaukar sababbin matakan tsaro domin tabbatar da cewa duk wata barazana ba ta samun gindin zama ba a jihar.

Kwamishinan yada labaran jihar ya ce za a cigaba da daukar matakai musamman a wuraren da ake zargin akwai waɗanda ba a san ko su waye ba.

Matakan tsaro da gwamnati ta ɗauka

A cewar sanarwar da ma’aikatar yaɗa labarai ta fitar, gwamnatin jihar ta tabbatar da cewa dukkan hukumomin tsaro suna kan aiki, tare da samun cikakken tallafi daga gwamnati.

Kara karanta wannan

Gwamna Abba Kabir ya ziyarci wuraren da aka yi artabu da 'yan bindiga a Kano

Sanarwar ta ce:

“Gwamnati za ta cigaba da tallafawa jami'an tsaro domin tabbatar da cewa sun samu nasara a aikinsu.”

Daily Post ta rahoto cewa an ce dukkan rundunonin tsaro a jihar sun fara tsaurara matakan da suka haɗa da saka idanu, sintiri da karfafa aikin bincike a dukkan kananan hukumomi 44.

Ana nazarin shawarwarin jama’a a Kano

Gwamnatin ta bayyana cewa tana yaba wa jama’a bisa shawarwarin da suke bayarwa, musamman game da tsaurara sa ido a manyan hanyoyin shiga da fita daga jihar.

An ce ana bin shawarwarin tare da mayar da su wani ɓangare na babban tsare-tsaren tsaro da ake gina wa jihar.

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Kano
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf. Hoto: Sanusi Bature D-Tofa
Source: Facebook

Gwamnatin ta yi kira ga mazauna Kano da su ci gaba da zama cikin nutsuwa, tare da kai rahoton duk wani abin da suka ga yana da yaƙini zai iya zama barazana ga tsaro.

Legit ta tattauna da Musa Adamu

Wani mazaunin Kano, Musa Adamu da ke zaune a 'Yan Kaba ya ce acaba ta dawo a Kano ne bayan saka dokar takaita zirga-zirgar adaidaita sahu.

Kara karanta wannan

An kama wasu 'yan kasashen waje da suka shigo Najeriya ta'addanci

'Na rasa ta ina aka samo babur Boxer a Kano, lokacin da ake acaba a baya da Jincheng ake yi.
"Yanzu haka nima ina da aiki, zan tashi wajen karfe 11:00 na dare. Idan na tashi ban san yadda zan yi na koma gida ba, dokar na shafan jama'a sosai."

Abba ya yi magana kan tsaron Kano

A wani labarin, kun ji cewa gwamnatin Kano ta ce barazanar tsaro da ake magana a kai ba wata babba ba ce a jihar.

Abba Kabir Yusuf ya ce ana yada jita-jita game da labaran da suke fitowa daga jihar a kan tsaro ko kai hare-hare.

Gwamnan ya bukaci al'umma su kwantar da hankulansu tare da cewa ana lura da kowane yanki na jihar Kano.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng