Yan Bindiga Sun Bukaci N150m Kudin Fansar Babban Sarki da Suka Sace

Yan Bindiga Sun Bukaci N150m Kudin Fansar Babban Sarki da Suka Sace

  • 'Yan bindigar da suka sace babban Sarki a Kwara sun kira iyalinsa da safe, suna neman miliyoyin kudin fansa kafin su sake shi
  • Basaraken ya bace ne a gonarsa, inda aka tsinci babur dinsa kawai, lamarin da ya tayar da hankalin mazauna yankin
  • Wani manomi daga wani kauye mai makwabtaka ya shaida cewa ya ga lokacin da ’yan bindigar suka yi awon gaba da Sarkin

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ilorin, Kwara - A karshe, bayan dogon jira, yan bindiga da suka sace Sarki a Kwara sun kira iyalansa domin neman kudin fansa.

'Yan bindiga da suka sace Ojibara na Bayagan, Oba Kamilu Salami a karamar hukumar Ifelodun ta jihar Kwara, sun tuntubi iyalinsa a yau Lahadi 30 ga watan Nuwambar 2025.

An bukaci N150m kudin fansar Sarki da aka sace
Taswirar jihar Kwara da ke fama da matsalolin tsaro. Hoto: Legit.
Source: Original

Rahoton Leadership ya ce maharan sun nemi Naira miliyan 150 a matsayin kudin fansarsa kafin su sake shi.

Kara karanta wannan

Ana wata ga wata: 'Yan bindiga sun tare hanya, sun sace matafiya a jihar Kogi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kwara: Yadda yan bindiga suka sace Sarki

An sace Oba Salami ne a gonarsa da misalin karfe 9:30 na safiyar Asabar 29 ga watan Nuwambar 2025 da muke ciki wanda ya jefa al'ummar yankin cikin matsala.

Al’ummar yankin sun tashi cikin tsananin firgici wasu da ake zargin masu garkuwa ne sun sace Sarkin Bayagan, jihar Kwara.

Shaidu sun bayyana cewa sun ga lokacin da ’yan ta'adda dauke da bindigogi suna tilasta wa sarkin hawa babur a gonarsa.

Har yanzu ba a tabbatar da adadin ’yan bindigar da suka kai harin ba, kuma ba su kira iyalan Sarki Kamilu Salami ba.

Yan bindiga sun bukaci N150m a matsayin kudin fansar Sarki
Oba Kamilu Salami da Sufeta-janar na yan sanda. Hoto: Nigeria Police Force.
Source: Facebook

Yan bindiga sun nemi N150m bayan sace basarake

Wani daga cikin iyalan basaraken ya bayyana cewa ’yan bindigar sun kira su da sanyin safiyar Lahadi 30 ga watan Nuwambar 2025 domin gabatar da bukatarsu.

Iyalan sun tabbatar da cewa maharan sun bukaci kudin fansa har Naira miliyan 150 domin sakin basaraken idan aka biya kudin ba tare da matsala ba.

Kara karanta wannan

Tashin hankali: 'Yan bindiga sun sace mai martaba sarki a jihar Kwara

Wasu daga cikin mutanen da ke da kusanci da basaraken sun tabbatar da cewa ’yan bindigar sun dira gonar, suka yi awon gaba da shi ba tare da wata takaddama ba.

Yadda lamarin ya jefa al'umma cikin fargaba

Hankalin jama’a ya fara tashi ne bayan wasu manoma da ke wurin suka gaza ganinsa, sai dai suka ga babur dinsa a ajiye a cikin gonar.

Wannan ya sa aka shiga neman sa a tsakanin mazauna kauyen wata majiyar yankin ya bayyana cewa wani manomi daga wani kauye na makwabtaka ya shaida da idanunsa yadda aka yi garkuwa da Sarkin.

Yan bindiga sun nemi kudin fansa N3bn

An ji cewa ’yan bindiga sun nemi kudin fansa Naira miliyan 100 ga kowane mutum daga cikin masu ibadar da suka sace a cocin CAC, Eruku.

A kalla mutane 30 zuwa 35 aka yi garkuwa da su yayin harin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane uku a wani yanki na jihar Kwara.

Biyo bayan lamarin, matasa sun gudanar da zanga-zanga, yayin da gwamnan jihar ya nemi karin matakan tsaro a yankin.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.