Majalisar Dattawa Ta Yi Magana da Allah Ya Yi Wa Sanata Rasuwa a cikin Dare

Majalisar Dattawa Ta Yi Magana da Allah Ya Yi Wa Sanata Rasuwa a cikin Dare

  • Ana ci gaba da tura sakon alhini da ta'aziyya bisa rasuwar Sanata mai wakiltar Enugu ta Arewa, Okechukwu Ezea na jam'iyyar LP
  • Majalisar dattawa ta bayyana jimamin wannan babban rashi, tana mai cewa marigayin ya ba da gudummuwa mai yawa a fannin dokoki
  • Ta mika sakon ta'aziyya ga al'ummar mazabar Enugu ta Arewa, gwamnatin Enugu, da iyalansa tare da addu'ar Allah ya ji kan Sanata Ezea

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Majalisar Dattawa ta bayyana alhini kan rasuwar Sanata Okechukwu Ezea (LP, Enugu ta Arewa), wanda ya rasu a daren Talata, 18 ga Nuwamba, 2025.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin yada labarai na majalisar dattawa, Sanata Adeyemi Adaramodu, ya fitar ranar Laraba a Abuja.

Majalisar Dattawa.
Hoton zauren Majalisar Dattawa da Marigayi Sanata Okechukwu Ezea Hoto: Okechukwu Ezea
Source: Facebook

Ya ce Najeriya ta yi babban rashi, domin marigayin yana daga cikin manyan ’yan majalisar dattawa da ke aiki a halin yanzu, kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Babbar magana: Sanatan Amurka ya taso gwamnati a gaba kan sace dalibai a Kebbi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar bayanin da iyalinsa suka fitar, Sanata Ezea ya rasu ne a asibiti mai zaman kansa a Legas, misalin ƙarfe 11:07 na dare, bayan gajeriyar rashin lafiya.

Majalisa ta jero alheran Sanata Ezea

Da yake mika sakon ta'aziyya a madadin majalisar, Adeyemi ya ce marigayi Sanata Ezea, wanda ya lashe zaben 2023 a inuwar LP, ya kasance mai tasiri a Majalisar Dattawa ta 10.

"A farkon majalisar ta 10 a 2023, ya shugabanci Kwamitin Ladabtarwa, Hakkoki da Korafe-korafe, kafin daga bisani ya koma jagorancin wasu manyan kwamitoci.
"Har zuwa lokacin rasuwarsa, shi ne Mataimakin Shugaban Kwamitin Hulɗa da Ci gaban Afirka da NEPAD kuma Mataimakin Shugaban Kwamitin Al’adu da Tattalin Arzikin Zamani.
"Ezea ya bar gado mai tasiri ta fuskar dokoki da muhawara a majalisa. Daga cikin manyan kudurorinsa akwai kafa Kwalejin Noma ta Tarayya, Adani, Kudirin kafa Jihar Adada."

Har ila yau, Sanata Adeyemi ya ce marigayin shi ne ya gabatar da kudirin da ya nemi a kafa sansanin soji a Karamar Hukumar Uzo-Uwani domin dakile hare-haren ’yan bindiga a yankin.

Kara karanta wannan

Duniya labari: Sanata mai ci a Najeriya ya rasu a Birtaniya yayin jinya

Majalisar Dattawa ta mika sakon ta'aziyya

A karshe dai Majalisar Dattawa ta ce tana mika sakon ta’aziyya ga al’ummar mazabar Enugu ta Arewa, gwamnatin jihar Enugu, da iyalan mamacin da kasa baki daya.

Ta kuma bayyana cewa Najeriya ta yi babban rashin mutum mai hangen nesa da taimakon al'umma, inda ta yi addu'ar Allah ya j ikan sa, in ji Leadership.

“Mun yi babban rashi, muna roƙon Allah Ya jikansa, Ya ba shi hutu madawwami," in ji Sanata Adeyemi Adaramodu.
Marigayi Sanata Ezea.
Hoton Sanatan Enugu ta Arewa da Allah ya yi wa rasuwa, Okechukwu Ezea Hoto: Okechukwu Ezea
Source: Facebook

Dan Agbese ya riga mu gidan gaskiya

A baya, kun ji labarin cewa babban dan jarida a Najeriya, Dan Agbese ya riga mu gidan gaskiya yana da shekaru 81 da haihuwa.

Agbese ya shahara wajen rubuce-rubuce masu tasiri kuma ya shafe shekaru masu ɗimbin yawa yana ba da gudunmawa a aikin jarida tun daga 1980.

Ana ganin dai rasuwarsa za ta bar babban gibi a harkar jarida, musamman ga waɗanda suka san shi a matsayin jagora kuma jajirtaccen edita.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262